Aminiya:
2025-12-13@08:27:32 GMT

Juventus ta kori kocinta Igor Tudor

Published: 28th, October 2025 GMT

Kungiyar ƙwallon ƙafa ta Juventus ta kori kocinta, Igor Tudor, bayan da ta sha kashi da ci 1-0 a hannun Lazio, lamarin da ya ba ta damar haɗa maki biyar kacal a wasanni biyar da ta buga a baya-bayan nan.

A cewar wata sanarwar da kulob ɗin ya fitar a ranar Litinin, Massimiliano Brambilla, wanda shi ne kocin tawagar maza ta farko, zai jagoranci Juventus a wasan da za ta kara da Udinese a ranar Laraba.

An raba wa iyalan ’yan sandan da suka mutu tallafin N31m a Jigawa Majalisar Dattawa za ta tantance sabbin hafsoshin tsaro ranar Laraba

“Juventus FC na sanar da cewa ta sallami Igor Tudor daga matsayin kocin tawagar maza ta farko, tare da sauran jami’ansa da suke taimaka masa a aikin horarswa — Ivan Javorcic, Tomislav Rogic da Riccardo Ragnacci,” in ji sanarwar.

Kulob ɗin ya gode wa Tudor da tawagarsa bisa kwazon da suka nuna a watannin da suka jagoranci kungiyar, yana yi musu fatan alheri kan duk lamuransu a nan gaba.

Yanzu haka Juventus tana mataki na takwas a teburin Serie A, da tazarar maki shida tsakaninta da Napoli wadda ke jan ragamar gasar.

A kofin Zakarun Turai na Champions League kuwa, Juve na matsayi na 25 cikin ƙungiyoyi 36 bayan ta yi canjaras ɗaya da kuma shan kashi a wasanni biyu na farko.

Tudor, tsohon ɗan wasan tsakiya na Croatia mai shekara 47, ya buga wasa da Juventus a lokacin yana murza leda, inda a watan Maris na bana kuma ya karɓi ragamar kulob ɗin daga hannun Thiago Motta.

Tun daga ranar 10 ga Satumban bana, Juventus ta buga wasanni takwas ba tare da samun nasara ba, ciki har da wasanni huɗu na bayan nan da ba ta zura ƙwallo ko ɗaya ba.

Alƙalumma sun nuna cewa Tudor ya samu nasara a wasanni 10 da ya jagoranci Juventus, sannan ya yi canjaras 8, da shan kashi sau shida.

Rahotanni na cewa wannan dai shi ne yanayi mafi muni da kulob ɗin ya fuskanta a baya-bayan nan, duk da cewa ya kashe euro miliyan 130 wajen cefanen ’yan wasa.

Daga cikin sabbin ’yan wasan da Juventus ta saya akwai Francisco Conceição, Nico González, Edon Zhegrova, da masu tsaron baya — Lloyd Kelly da Piere Kalu. Sai kuma Loïs Openda da ta ɗauko aro da Jonathan David da kulob ɗin ya ɗauko kyauta.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Zan yi amfani da Salah a wasan Liverpool da Brighton — Arn Slot

Mai horar da Ƙungiyyar Ƙwallon Ƙafa ta Liverpool, Arne Slot ya ce zai sanya Mohammed Salah cikin jerin ’yan wasan da za su bugawa Liverpool wasa da Brighton a ranar Asabar.

Slot wanda ya samu saɓani da Salah kan ajiye shi a benci a wasanni uku a jere, ya ce yana da yaƙinin cewa, Salah zai ci gaba da bugawa ƙungiyar wasa.

2027: Jam’iyyar NNPP ta rantsar da sabbin shugabanni a Gombe Osimhen ya lashe kyautar gwarzon ɗan wasan bana na Turkiyya

Ya kuma ƙara da cewa, zai ci gaba da tattaunawa da ɗan wasan domin ya ci gaba da taka leda a Anfield.

Salah mai shekara 33, baya cikin jerin ‘yan wasan da suka doke Inter Milan a Italiya a ranar Talata, wanda hakan ke bayyana tsamin rashin jituwa tsakaninsa da Arne Slot.

Liverpool dai zata karɓi baƙuncin Brighton a wasan mako na 16 da ƙarfe 3 na ranar Asabar.

Mo Salah, ɗan asalin ƙasar Masar, ya bugawa Liverpool wasanni 420 tare da zura ƙwallaye 250 cikin zamansa a ƙungiyyar.

Ɗan wasan zai bar Liverpool domin dawowa ƙasar Masar a ranar 15 ga watan Disamba, kwanaki 6 gabanin fara kofin nahiyyar Afrika da ƙasar Morocco zata karɓi baƙunci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kotu ta sa ranar yanke hukunci a Shari’ar Abba Kyari da NDLEA
  • Zan yi amfani da Salah a wasan Liverpool da Brighton — Arn Slot
  • 2027: Jam’iyyar NNPP ta rantsar da sabbin shugabanni a Gombe
  • Osimhen ya lashe kyautar gwarzon ɗan wasan bana na Turkiyya
  • Matatar man Dangote ta rage farashin fetur zuwa N699
  • NLC Ta Shirya Zanga-Zangar Rashin Tsaro A Faɗin Ƙasa Ranar 17 Ga Disamba
  • Osimhen Ya Lashe Kyautar Gwarzon Dan Wasan Kwallon Kafa Na Bana A Kasar Turkiyya
  • Jam’iyyar PDP ta tabbatar da mutuwar mataimakin Gwamnan Bayelsa
  • Zanga-zanga ta ɓarke bayan haɗarin tirela ta kashe mutum a Yobe
  • Borkina Faso Ta Saki Sojojin Sama Na Najeriya 11 Da ta Kama Bayan Jirginsu Yayi Saukar Gaggawa.