Ba zan sake tsayawa takara ba, zan bai wa matasa dama — Dasuki
Published: 26th, October 2025 GMT
Ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar mazaɓar Kebbe/Tambuwal, Abdussamad Dasuki, ya ce ba zai tsaya takara a zaɓen 2027 ba.
Dasuki, ya ce ya ɗauki wannan mataki ne domin bai wa matasan Najeriya damar shiga harkokin mulki.
El-Clasico: Real Madrid ta doke Barcelona da ci 2 Majalisa ta amince a ƙirƙiro sabbin jihohi 6 a NajeriyaYa bayyana cewa tun daga shekarar 2011 yake majalisar dokoki, kuma yana ganin zai fi dacewa idan aka bai wa matasa dama a dimokuraɗiyya.
“Najeriyar da muke mafarki za ta tabbata ne kawai idan mun yi sadaukarwa,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa bayan tuntuɓar iyalansa da jagororinsa, ya yanke shawarar bai zai sake tsayawa takara ba don ya gaji ba, sai don bai wa wasu dama.
Dasuki dai shi ne shugaban riƙon kwarya na ƙungiyar ‘Future Is Now Project’, ƙungiyar da ke fafutukar ganin an dama da matasa a harkokin siyasa.
An ƙaddamarda ƙungiyar a ranar 1 ga watan Oktoba, 2025 a Abuja.
Ƙungiyar ta buƙaci cewa a zaɓen 2027, kashi 70 cikin 100 na kujerun majalisar wakilai su kasance a hannun matasa ’yan kasa da shekaru 40.
Ya ce ko da yake shi ma matashi ne duk da ya haura shekaru 40, don haka dole ya gwada misali da kansa.
“Idan muna son ganin matasa sun jagoranci ƙasar nan, dole mu nuna hakan a aikace, Wannan ita ce sadaukarwa. Idan na matsa gefe sabbin jagorori za su fito,” in ji shi.
Shawarar Dasuki ta zama abun a yaba, a siyasar Najeriya, domin ba kasafai ake samun ’yan siyasa suna hakura da kujerunsu don raɗin kansu ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗan Siyasa Zaɓe
এছাড়াও পড়ুন:
Sakkwatawa na murnar kisan da sojoji suka yi wa mataimakin Bello Turji
Al’ummar ƙaramar hukumar Sabon Birni da ke jihar Sakkwato sun bayyana farin ciki bayan samun labarin kashe fitaccen ɗan bindiga da ya dade yana addabar yankin gabashin jihar, Kacalla Kallamu.
Rundunar Sojoji ta 8 ta hallaka jagoran ’yan bindiga, Kachalla Kallamu, a wani samamen haɗin gwiwa da aka kaddamar a ƙaramar hukumar Sabon Birni.
Dalibin jami’a ya rasu a hatsarin motar murnar kammala jarabawa Iya sojojin da ke tsaron Seyi Tinubu sun isa su samar da tsaro a Benin – SoyinkaWata majiyar soja da ta tabbatar da lamarin ga manema labarai a ranar Talata ta bayyana samamen a matsayin “babbar asara ga cibiyar ’yan bindigar Bello Turji,” tana mai cewa Kallamu shi ne babban na hannun daman Turji.
A cewar majiyar, an kashe Kallamu tare da wani daga cikin manyan masu samar wa Turji kayayyakin aiki a lokacin samamen da aka gudanar da safe a kauyen Kurawa ranar Litinin.
Majiyar ta ƙara da cewa aikin ya samu muhimmiyar gudunmuwar kungiyoyin sa‑kai na yankin.
“Mun dade muna bibiyar Kallamu. Kashe shi wata babbar nasara ce wajen raunana karfin ’yan bindigar da ke Sabon Birni da kewaye,” in ji majiyar.
Mamacin, wanda asalin ɗan Garin Idi ne a Sabon Birni, ya dade yana addabar al’ummar yankin.
Ana zargin ya gudu zuwa Jihar Kogi bayan ya tsere wa luguden wutar sojoji a watan Yuni 2025, amma ya sake shigowa yankin kwanan nan ba tare da an sani ba.
Majiyar ta yaba da ƙarin bayanan sirri da ake samu daga al’ummomin yankin, tana mai cewa haɗin kai tsakanin mazauna yankin da jami’an tsaro ya taka muhimmiyar rawa wajen nasarorin baya‑bayan nan.
Manema labarai sun ruwaito cewa an ci gaba da murnar labarin a Sabon Birni, yayin da mashawarcin musamman ga Gwamna Ahmad Aliyu kan harkokin tsaro, Kanal Ahmed Usman (mai ritaya), ya yaba wa dakarun bisa “ci gaba da jajircewa da ƙwarewa” wajen yaƙi da ’yan bindiga.
Mutanen garin Sabon Birni sun fito maza da mata suna murnar nasarar da aka samu, har suna cewa suna jin wannan rana kamar ta Sallah.
Sun yi fatan a ci gaba da samun nasarori irin wannan domin kawar da ’yan bindiga a yankin, a jihar, da kuma Arewacin Najeriya gaba ɗaya.