Asalin tsarin shari’ar da ake amfani da shi game da kare muradun al’umma ya bai wa masu gabatar da kara damar yin aiki na neman hukunta masu laifi a madadin sauran al’umma a shari’o’in da suka shafi laifukan gurbata muhalli, da rashin kiyaye tsaftar abinci, da kuma rashin da’a ga gwamnati wadanda dukkansu idan aka bar su kara-zube, za su tauye hakkokin galibin jama’a.

Amma a halin yanzu, sabon daftarin dokar da ake son kafawa ya fayyace nau’ikan dokoki 16, ciki har da karin wasu muhimman abubuwa guda biyu da suka shafi al’adun gargajiya da kuma tsaron kasa, wanda ke nuna kara fadada tsarin dokar.

 

Domin ganin ba a tauye hakkin kowane bangare tsakanin mahukunta da mabiya ba, a karkashin daftarin dokar, dole ne masu gabatar da kara su fara gabatar da bukatar hukumomin gwamnati da su sauke nauyin da ke wuyansu kafin shigar da kara a kansu. A bangaren kare hakkin jama’a kuma, an haramta daukar matakan tilastawa kamar hana mutum amfani da asusunsa na banki da kadarori ko takaita ‘yancin walwala a yayin gudanar da bincike. Kazalika, an karfafa gwiwar ‘yan kasa da kungiyoyin kyautata zamantakewa su bayar da rahoton keta hakkokin jama’a da kuma sa ido kan shari’o’in da ake gudanarwa kan hakan.

 

Daga shekarar 2015 zuwa 2025, hukumomin da ke kula da share hawayen jama’a a bangaren shari’a sun yi aiki a kan korafe-korafe fiye da miliyan 1.22 wadanda galibi aka gabatar a kan ma’aikatun gwamnati.

 

Su dai tsare-tsaren da ake amfani da su na kare muradun jama’a a kasar Sin ba a tattare suke a wuri guda ba, suna warwartse ne a karkashin dokokin gudanarwa na fararen hula daban-daban, amma wannan daftari ya hade su wuri guda.

 

Kokarin tabbatar da wannan daftarin doka na kare muradun al’umma a kasar Sin, babu shakka ya kara fito da burin kasar na gyare-gyare a dukkan fannoni tare da cike gibin da ake ganowa, yayin da kasar ta hau turbar cimma burin zamanintarwa a karkashin tsarin gurguzu nan da shekarar 2035. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Binciken ‘Yan Sanda Kan Wanda Ake Zargi Da Tawayen “‘Yancin Kan Taiwan” Mataki Ne Na Adalci Don Kare Hadin Kan Kasa October 29, 2025 Daga Birnin Sin Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump October 29, 2025 Daga Birnin Sin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba October 28, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

 

Idan muka kwatanta da kasar Sin, sabanin yawan albarkatun da Afrika ke da su kamar na kasar noma, ita Sin kasa da kaso 9 kadai take da shi, amma kuma tana bayar da gagagrumar gudunmawa a duniya, inda take tsaye da kafarta wajen ciyar da al’ummarta, har ma ta bayar da gudunmawa ga kasashe mabukata.

 

To mene ne dalilin nasarar Sin a wannan bangare?

Gaggarumar nasarar da Sin ta samu a bangaren aikin gona, ba wani abu ba ne illa jajircewar gwamnatin kasar da dabaru da fasahohin aikin gona da kullum ake lalubowa. Misali, ko a cikin hamada, kasar Sin ta lalubo dabarun da suka dace, inda ake noman tsirrai masu juriya dake iya ciyar da mutane da samar da kudin shiga tare da yaki da kwararar hamada. Haka kuma, fasahohinta na samar da ingantattun iri da noma cikin daki ko rumfa, duk abubuwa ne da suka bunkasa yabanya a kasar. Ga uwa uba kayayyakin aiki na zamani da manomanta ke amfani da su. Za mu iya bayyana aikin gona a kasar Sin a matsayin wata sana’a ta zamani sabanin yadda ake ganinta a matsayin sana’a mai wahala da bata samar da kudin shiga.

 

La’akari da yawan jama’a da yadda ta kasance koma baya, tabbas nahiyar Afrika na bukatar fasahohin Sin domin fitar da al’ummominta daga kangin talauci tare da wadatar da su da abinci. Dabaru da fasahohin Sin, za su yi wa bangaren aikin gona a nahiyar gagarumin garambawul, domin idan aka tabbatar da hada fasahohin da tarin albarkatun da nahiyar take da su, to kasashen Afrika za su iya tsayawa da kafarsu, su kuma fatattaki yunwa da talauci, da karfafa gwiwar matasa ta yadda za su rika ganin aikin gona a matsayin wata sana’a mai riba. Tabbas ingantattun fasahohin aikin gona na Sin, za su taka rawar gani wajen kyautata makomar nahiyar Afrika. (Fa’iza Mustapha)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Xi Ya Yi Karin Haske Kan Muhimman Shawarwarin Da Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Yayin Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 October 28, 2025 Daga Birnin Sin An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka October 27, 2025 Daga Birnin Sin Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani October 27, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya janye afuwar da ya yi wa Maryam Sanda da masu manyan laifuka
  • Iraki: Al-Sudani ya kirayi Irakawa da suka kare kundin tsarin Mulki ta hanyar fitowa zabe
  • Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba
  • Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin
  • Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika
  • ’Yan bindiga sun sa harajin N15m kan al’ummar Mazabar Sanata Tambuwal
  • Al-Burhan: Sojojin Sudan Sun Janye Daga El-Fasher Saboda Kare rayukan Fararen Hula
  • Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu
  • Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa