Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a
Published: 29th, October 2025 GMT
Asalin tsarin shari’ar da ake amfani da shi game da kare muradun al’umma ya bai wa masu gabatar da kara damar yin aiki na neman hukunta masu laifi a madadin sauran al’umma a shari’o’in da suka shafi laifukan gurbata muhalli, da rashin kiyaye tsaftar abinci, da kuma rashin da’a ga gwamnati wadanda dukkansu idan aka bar su kara-zube, za su tauye hakkokin galibin jama’a.
Domin ganin ba a tauye hakkin kowane bangare tsakanin mahukunta da mabiya ba, a karkashin daftarin dokar, dole ne masu gabatar da kara su fara gabatar da bukatar hukumomin gwamnati da su sauke nauyin da ke wuyansu kafin shigar da kara a kansu. A bangaren kare hakkin jama’a kuma, an haramta daukar matakan tilastawa kamar hana mutum amfani da asusunsa na banki da kadarori ko takaita ‘yancin walwala a yayin gudanar da bincike. Kazalika, an karfafa gwiwar ‘yan kasa da kungiyoyin kyautata zamantakewa su bayar da rahoton keta hakkokin jama’a da kuma sa ido kan shari’o’in da ake gudanarwa kan hakan.
Daga shekarar 2015 zuwa 2025, hukumomin da ke kula da share hawayen jama’a a bangaren shari’a sun yi aiki a kan korafe-korafe fiye da miliyan 1.22 wadanda galibi aka gabatar a kan ma’aikatun gwamnati.
Su dai tsare-tsaren da ake amfani da su na kare muradun jama’a a kasar Sin ba a tattare suke a wuri guda ba, suna warwartse ne a karkashin dokokin gudanarwa na fararen hula daban-daban, amma wannan daftari ya hade su wuri guda.
Kokarin tabbatar da wannan daftarin doka na kare muradun al’umma a kasar Sin, babu shakka ya kara fito da burin kasar na gyare-gyare a dukkan fannoni tare da cike gibin da ake ganowa, yayin da kasar ta hau turbar cimma burin zamanintarwa a karkashin tsarin gurguzu nan da shekarar 2035. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
Ansarallah: Dole Ne Kasar Yemen Ta Tsarin Musulunci Na Kaiwa Ga Daukaka
Shugaban kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen Sayyid Abdulmalik Badruddeen Huthi ya bayyana cewa dole ne musulman kasar Yemen maza da mata sun bi tafarkin addinin musulunci na kaiwa ga daukaka idan suna son daukaka.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran nakalto Al-Huthi yana fadar haka a jiya Laraba da yamma a lokacinda yake magana kan zagayowar ranar haihuwar Fatimah Azzahra diyar manzon Allah (s).
Malamin ya kara da cewa, Fatimah (a) abin koikoyo ne ga dukkan musulmi maza da mata a sanin Allah da halaye masu kyau don samun kusance ga Allah madaukakin sarki.
Al-Huthi ya kara da cewa a halin yanzu musulmi a ko ina suke a duniya suna fuskantar matsaloli, musamman musulman kasar Falasdinu wadanda HKI ta kashe dubban mutane daga cikinsu a cikin yan shekaru da suka gabata. Sun kashe mata da maza yara kanana hatta wadanda suke cikin iyayensu basu barsu ba.
Ya ce mafita ga musulmi itq ce koyi da iyalan gidan manzon Allah (s) musamman Fatima (a) don samun guzurin samun karfin fuskantar makiya a ko ina suke.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugaban Iran Ya Isa Astana Babban Birnin Kazakhstan December 11, 2025 ECOWAS ta bukaci waware batutuwa na siyasa ta hanyoyin lumana a yammacin Afirka December 11, 2025 Reuters: Amurka na matsa lamba kan kotun ICC don janye bincike kan yakin Gaza da Afghanistan December 11, 2025 Ghana ta yi Allah wadai da cin mutuncin ‘yan kasarta da ke balaguro a Isra’ila December 11, 2025 Sakamkon Jin Ra’ayi: Yawancin Amurkawa na adawa da kai hari kan Venezuela December 11, 2025 Hamas Ta yi Tir Da Sabbin Matsugunan Yahudawa Da Isra’ila Ke yi A Yankunan Da Ta Mamaye December 10, 2025 Kasashen Nijeriya Da Saudiyya Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Tsaro Ta Shekaru 5 December 10, 2025 Shugaban Kasar Iran Yace Mata Su ne Ginshin Gina Makomakar Kowacce Kasa December 10, 2025 Iran Ta yi Tir Da Kisan Karen Dangin Isra’ila A Gaza A Ranar Yaki Da Kisan Kiyashi Ta MDD December 10, 2025 Borkina Faso Ta Saki Sojojin Sama Na Najeriya 11 Da ta Kama Bayan Jirginsu Yayi Saukar Gaggawa. December 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci