Leadership News Hausa:
2025-10-30@23:12:10 GMT

Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

Published: 30th, October 2025 GMT

Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

 

Matsalar, kamar ko yaushe, ita ce gaskiyar cewa Osimhen ba zai yi arha ba kuma Barcelona za ta yi fama da biyan manyan “yan wasa a bazara mai zuwa, Julian Alvarez da Erling Haaland sun riga sun kasance cikin wadanda kungiyar ta Catalonia ta fara nema, yayin da kuma ta ke kallon Etta Eyong da Serhou Guirassy na Borrusia Dortmund.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi October 28, 2025 Wasanni El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid October 26, 2025 Wasanni Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru October 26, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan kasuwar duwatsu masu daraja na ɗaukar nauyin ta’addanci —EFCC

Hukumar Yaƙi da Masu Karya Tattalin Arziki (EFCC) ta bayyana damuwa kan yadda wasu ’yan kasuwar duwatsu masu tsada a Najeriya ke cikin wadanda ake zargin suna taimakawa wajen daukar nauyin ta’addanci a sassan Najeriya.

Hukumar ta gargaɗe su da masu hakar ma’adinai da su guji zama hanyar safarar kuɗaɗen haram ko tallafa wa ƙungiyoyin ta’addanci ta kowace hanya, tana mai jan hankalinsu da su daina harkokin da ke hana ci gaban tattalin arziki da tsaro a ƙasar.

Shugaban EFCC, Ola Olukoyede, ne ya faɗi haka a Ibadan, hedikwatar Jihar Oyo, yayin taron wayar da kai da horaswa na rana ɗaya da aka shirya domin masu haƙar ma’adinai da ’yan kasuwar duwatsu masu tsada a jihar.

Taron ya samu haɗin gwiwa tsakanin EFCC da Hukumar Bayar da Bayanai kan Harkokin Kuɗi (NFIU) tare da tallafin GIZ, wata cibiyar haɗin gwiwar Jamus.

Jami’an tsaro sun kashe ’yan bindiga 80 a Kebbi Rikicin ADC: Sanata Nenadi ta zama shugaba a Kaduna

Olukoyede, wanda ya bayyana takaicinsa kan halayen wasu ’yan kasuwar, ya ce akwai “ tsananin rashin kula” daga ɓangaren masu haƙar ma’adinai da ’yan kasuwar duwatsu masu tsada, musamman wajen bin dokar sanin abokin hulɗa (KYC).

Ya koka kan yadda ake kin bayar da rahoton mu’amaloli masu alamun shakku, yana mai cewa hakan na kawo cikas ga yunkurin EFCC wajen yaƙi da safarar kuɗaɗen haram da kuma tallafin ta’addanci a Najeriya.

Shugaban EFCC ya yi wannan jawabi ne ta bakin Toyin Ehindero-Benson, Kwamandan Ofishin Kula da Safarar Kuɗaɗen Haram (SCUML) na shiyyar Ibadan, inda ta buƙaci mahalarta taron su koyi cikakkun ƙa’idojin da ke jagorantar ayyukan SCUML.

Ta ce hakan zai taimaka musu wajen fahimtar nauyin da ke kansu da kuma bin ƙa’idojin yaƙi da safarar kuɗaɗe da kuma hana ɗaukar nauyin ta’addanci, musamman ma a matsayinsu na manyan masu ruwa da tsaki a fannin haƙar ma’adinai.

A cewar sanarwar da kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya fitar, Olukoyede ya bayyana cewa: “Halin wannan fanni na haƙar ma’adinai yana sanya shi zama muhimmin ɓangare a yaƙi da laifukan kuɗi.

“Wannan taro kuma wata dama ce ta musayar ra’ayoyi, faɗakarwa, da ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin hukumomi da masu ruwa da tsaki.”

A nasa jawabin, Michael Etuk, Mataimakin Shugaban Ƙungiyar ’Yan Kasuwar Duwatsu Masu Tsada ta Ojoo, Jihar Oyo, ya tabbatar wa EFCC cewa ’yan kasuwa da masu haƙar duwatsu a jihar za su yi duk abin da doka ta tanada domin taimaka wa gwamnati wajen ƙarfafa yaƙi da safarar kuɗaɗen haram da kuma ɗaukar nauyin ta’addanci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƙwallo ta kashe ɗan wasan Cricket
  • Iran ta yi fatali da kalamman IAEA Kan Shirin Nukiliyarta
  • Ƙungiyar Rays Heaven ta Ƙarfafa Wayar da Kai kan Lafiyar Kwakwalwa a Kaduna
  • Kamfanin Amazon na shirin sallamar ma’aikata 600,000 don maye gurbinsu da mutum-mutumi
  • Majalisa ta amince Tinubu ya karɓo rancen dala biliyan 2.35
  • Jami’ar MDD Ta Musamman A Falasdinu Ta Soki Shirin Trump Kan Tsagaita Bude Wuta A Gaza
  • Juventus ta kori kocinta Igor Tudor
  • Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi
  • ’Yan kasuwar duwatsu masu daraja na ɗaukar nauyin ta’addanci —EFCC