Aminiya:
2025-10-29@00:02:13 GMT

Amurka ta soke bizar Wole Soyinka

Published: 28th, October 2025 GMT

Fitaccen marubucin nan ɗan Nijeriya wanda ya taɓa lashe kyautar Nobel, Farfesa Wole Soyinka, ya ce gwamnatin Amurka ta soke bizarsa tana mai haramta masa shiga ƙasar.

Farfesa Soyinka ya bayyana hakan ne a yayin wani taron manema labarai da ya kira a Legas a ranar Talatar nan.

Netanyahu ya ba da umarnin kai mummunan farmaki a Gaza Juventus ta kori kocinta Igor Tudor

Ya bayyana cewa Ofishin Jakadancin Amurka ne ya sanar da shi batun ƙwace bizar a wata wasiƙa da ya aike masa.

Sai dai ya sanar da cewa ba shi da masaniya kan wani mummunan laifi da ya aikata da har zai sa Amurkan ta soke bizar da ta ba shi.

“Ya zama dole ne na kira wannan taron saboda mutanen Amurka da ke tsammanin zuwana wasu taruka da cewa kar su ɓata lokacinsu.

“Ba ni da biza; an haramta min shiga Amurka. Saboda haka idan kuna son ganina, kun san inda za ku same ni,” in ji Soyinka.

“Har yanzu ina bibiyar tarihina na baya… Ba ni da wani tarihin aikata laifuka a baya ko ma babban laifi ko rashin ɗa’a da zai sa in cancanci a soke min biza.

“Na fara waiwayen baya—shin na taɓa yi wa Amurka wani rashin adalci? Shin ina da wani mugun tarihi? An yanke min hukunci? Shin na saɓawa wata doka a ko’ina?”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Farfesa Wole Soyinka

এছাড়াও পড়ুন:

Ba zan sake tsayawa takara ba, zan bai wa matasa dama — Dasuki

Ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar mazaɓar Kebbe/Tambuwal, Abdussamad Dasuki, ya ce ba zai tsaya takara a zaɓen 2027 ba.

Dasuki, ya ce ya ɗauki wannan mataki ne domin bai wa matasan Najeriya damar shiga harkokin mulki.

El-Clasico: Real Madrid ta doke Barcelona da ci 2 Majalisa ta amince a ƙirƙiro sabbin jihohi 6 a Najeriya

Ya bayyana cewa tun daga shekarar 2011 yake majalisar dokoki, kuma yana ganin zai fi dacewa idan aka bai wa matasa dama a dimokuraɗiyya.

“Najeriyar da muke mafarki za ta tabbata ne kawai idan mun yi sadaukarwa,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa bayan tuntuɓar iyalansa da jagororinsa, ya yanke shawarar bai zai sake tsayawa takara ba don ya gaji ba, sai don bai wa wasu dama.

Dasuki dai shi ne shugaban riƙon kwarya na ƙungiyar ‘Future Is Now Project’, ƙungiyar da ke fafutukar ganin an dama da matasa a harkokin siyasa.

An ƙaddamarda ƙungiyar a ranar 1 ga watan Oktoba, 2025 a Abuja.

Ƙungiyar ta buƙaci cewa a zaɓen 2027, kashi 70 cikin 100 na kujerun majalisar wakilai su kasance a hannun matasa ’yan kasa da shekaru 40.

Ya ce ko da yake shi ma matashi ne duk da ya haura shekaru 40, don haka dole ya gwada misali da kansa.

“Idan muna son ganin matasa sun jagoranci ƙasar nan, dole mu nuna hakan a aikace, Wannan ita ce sadaukarwa. Idan na matsa gefe sabbin jagorori za su fito,” in ji shi.

Shawarar Dasuki ta zama abun a yaba, a siyasar Najeriya, domin ba kasafai ake samun ’yan siyasa suna hakura da kujerunsu don raɗin kansu ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu
  • An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka
  • Amurka ta tsare wani dan jarida musulmi saboda sukar Isra’ila
  • “Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”
  • Ba zan sake tsayawa takara ba, zan bai wa matasa dama — Dasuki
  • Sin Da Amurka Sun Cimma Matsaya Dangane Da Tsare-Tsaren Warware Batutuwan Cinikayya Da Suke Mayar Da Hankali A Kai
  • Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Ce: Shugaban Amurka Zai Ci Gaba Da Kasancewa Cikin Rudu
  • An kama mutum 25 kan zargin shirya auren jinsi a Kano