Leadership News Hausa:
2025-10-26@22:41:25 GMT

“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

Published: 26th, October 2025 GMT

“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

Shugaban ƙungiyar ta ƙasa, Frank Ogunojemite, ne ya sanya rattaba hannunsa a wasiƙar kamar yadda Jaridar PUNCH, ta samu kwafinta.

Shugaba ya bayyana cewa, ya kafa hujjar buƙatar soke tsarin, kan ƙalubalen da take fuskanta, na kashe kuɗaɗe masu yawa, musamman wajen safarar mayan Kwantainonin da ake shigoa da su daga ƙasashen da ke a Afirka ta Yamma

Ya ce, wannan tsarin ya sanya a yanzu, ana yiwa  masu safarar kaya zuwa cikin Tashar wani sabon cajin kuɗi da kuma jinkirin da suke samu, wajen shigar da kayan zuwa cikin Tashar.

Ogunojemite ya buƙaci Hukumar da ta tabbatar da wanzar da tsarin a matsayin na bai ɗaya a ɗaukacin Tashishin Jiragen Ruwan ƙasar.

“Muna gabatar da wannan buƙatar ce, domin mun yi amanna da cewa, a ƙarƙashin shuganacin shugaban Hukumar zai ci gaba da yin adalci da kuma tabbatar da ana bin ƙa’ida da kuma yin dubi ga lamarin ci gaban ƙasar nan, kan abinda ya shafi tafiyar da harkokin Jiragen Ruwan ƙasar,” Inji  Ogunojemite.

“A shirye muke domin yin tattaunawa da Hukumar da kuma sauran hukomin da abin ya shafa domin a lalubo da mafita, kan wannan buƙatar ta mu.” A cewar shugaban.

Sai dai, a martanin da Onyemekara ya jaddada cewa, babu gudu ba bu ja da baya na dakatar da wannan tsarin.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano October 26, 2025 Manyan Labarai Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025, Dakta Zacch Adedeji October 26, 2025 Labarai Gwamnonin Arewa Sun Jajanta Wa Jihar Neja Kan Fashewar Tankar Mai October 26, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisa ta amince a ƙirƙiro sabbin jihohi 6 a Najeriya

Kwamitin Haɗin Gwiwa na Majalisar Dattawa da Majalisar Wakilai kan gyaran kundin tsarin mulkin Najeriya, ya amince da buƙatar ƙirƙiro sabbin jihohi guda shida.

Wannan mataki na cikin abin da aka cimma a ƙarshen taron kwana biyu da aka gudanar a Legas, ƙarƙashin jagorancin Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, da Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai, Benjamin Kalu.

Matsalar kashe-kashe a Nijeriya ba ta da alaƙa da addini — Femi Kayode Boko Haram na amfani da jirage marasa matuƙa wajen kai hare-hare — Zulum

A cewar kwamitin, an tattauna kan buƙatu 69, ciki har da buƙatun ƙirƙirar jihohi 55 da kuma ƙananan hukumomi 278.

Daga cikin buƙatun ƙirƙirar jihohi 55 da aka gabatar, kwamitin ya amince da ƙirƙirar jihohi shida; ɗaya daga kowanne yanki.

“Za mu binciki dukkanin buƙatun ƙirƙirar jihohi 55 da aka gabatar domin gano inda za a fitar da sababbin jihohi shida.

“Za mu yi wa kowa adalc,” in ji ɗaya daga cikin mambobin kwamitin daga yankin Arewa Maso Yamma.

Idan Majalisar Tarayya ta amince da wannan yunƙuri gaba ɗaya, Najeriya za ta koma tana da jihohi 42 maimakon 36 da ake da su yanzu.

Wannan mataki, a cewar wani babban jami’in majalisar, “Yana nuna adalci da daidaito ga dukkanin yankuna,” kuma za a gabatar da rahoton kwamitin ga duka majalisun a farkon makon Nuwamba.

Sanata Barau, ya ce burin majalisar shi ne tabbatar da cewa duk wasu sauye-sauye da za a yi wa kundin tsarin mulki su kasance waɗanda za su amfani al’umma, tare da cika alƙawarin da aka ɗauka na tura sabon ƙudiri zuwa majalisun dokoki na jihohi kafin ƙarshen wannan shekara.

“Mun shafe sama da shekaru biyu muna taro da al’umma, ƙungiyoyi, da masana domin samun ra’ayoyi game da yadda za a inganta tsarin mulkin ƙasar nan,” in ji shi.

Taron na Legas ya kasance dama ga mambobin majalisar domin su nazarci sauye-sauyen da ake son yi, musamman batutuwan da suka shafi ƙirƙirar sabbin jihohi, daidaita iyakoki, da ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya
  • Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025, Dakta Zacch Adedeji
  • Majalisa ta amince a ƙirƙiro sabbin jihohi 6 a Najeriya
  • Muna Duba Ƙudirin Ƙirƙiro Jihohi 55 – Barau Jibrin
  • Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci
  • Ƙungiyoyin Ma’aikatan Jihar Kaduna Sun Yabawa Gwamna Sani Kan Amincewa Da Sabon Albashin  Ma’aikata
  • Majalisar Tattalin Arziki Ta Amince da Shirin Gyara Cibiyoyin Horar da Jami’an Tsaro
  • Buƙatar Daƙile Badaƙalar Amfani Da Takardun Karatun Bogi A Nijeriya
  • Tinubu ya bukaci sabon shugaban INEC ya gudanar da zaben gaskiya a 2027