Rahotonni sun bayyana ɓarkewar zanga-zanga a birnin Douala, cibiyar kasuwancin Kamaru jim kadan bayan sanar da sakamakon zaɓen shugaban ƙasar.
Wasu bidiyoyi da aka yaɗa a dandalan sada zumunta sun nuna gomman mutane sun fantsama kan titunan birnin, tare da rera waƙoƙin goyon bayan Issa Tchiroma Bakary, jagoran adawar ƙasar.
Kamfanin dillancin labaran Kamaru, ya wallafa wani bidiyo da ke nuna yadda aka lalata wani ginin majalisar birnin, bayan da masu zanga-zangar suka far masa.
BBC ya ruwaito cewa, a yayin da ake ci gaba da zaman ɗar-ɗar kan abin da ka iya faruwa bayan sanar da sakamakon zaɓen Kamaru, makarantu da shaguna sun kasance a rufe a Yaoundé, babban birnin ƙasar.
Hatta ma’aikatan gwamnati da dama sun ƙi fita wuraren ayyukansu saboda fargabar abin da ka iya biyo bayan sanar da sakamakon zaɓen.
Sai dai rahotanni sun nuna cewa girke jami’an tsaro masu yawa a manyan birane, musamman Yaoundé, Douala da kuma Garoua, mahaifar jagoran adawa Tchiroma Bakary, ya taƙaita zanga-zangar da aka fara gudanarwa.
Kawo yanzu, yawancin ‘yan ƙasar sun ci gaba da kasancewa a cikin gidajensu bayan da aka bayyana Shugaba Paul Biya a matsayin wanda ya lashe zaɓen, wanda hakan ke tabbatar masa da wa’adin mulki na takwas.
Shugaba Paul Biya shi aka sanar a hukumance a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa karo na takwas a cewar Kotun Tsarin Mulkin Kamaru, yayin da tun farko jagoran ’yan adawa Issa Tchiroma Bakary ya ayyana kansa a matsayin wanda ya yi nasara.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kamaru
এছাড়াও পড়ুন:
Za a Yi wa Yara 194,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Karamar Hukumar Birnin Kudu
Karamar hukumar Birnin Kudu dake Jihar Jigawa ta bada tabbacin ci gaba da kulawa da harkokin rigakafi da kiwon lafiya baki daya.
Shugaban karamar hukumar, Builder Muhammad Uba ne ya bada wannan tabbacin lokacin taro da ake gudanarwa a kowace rana kan al’amuran rigakafin cutar Polio da aka gudanar a fadar Hakimin Birnin kudu.
Yace karamar hukumar zata kara da bada fifiko wajen tallafawa harkokin rigakafi domin dakile yaduwar cututtuka a yankin.
A don haka, Builder Muhammad Uba ya bukaci iyaye su kara himma wajen bada hadin kai da goyon baya ga jami’an lafiya a duk lokacin da ake gudanar da rigakafi.
A jawabin da ya gabatar mai kula da al’amuran rigakafi na yankin, Malam Abubakar Alhassan Garki yace ana sa ran yiwa kananan yara 194,000 rigakafin cutar shan inna a karamar hukumar.