Rahotonni sun bayyana ɓarkewar zanga-zanga a birnin Douala, cibiyar kasuwancin Kamaru jim kadan bayan sanar da sakamakon zaɓen shugaban ƙasar.
Wasu bidiyoyi da aka yaɗa a dandalan sada zumunta sun nuna gomman mutane sun fantsama kan titunan birnin, tare da rera waƙoƙin goyon bayan Issa Tchiroma Bakary, jagoran adawar ƙasar.
Kamfanin dillancin labaran Kamaru, ya wallafa wani bidiyo da ke nuna yadda aka lalata wani ginin majalisar birnin, bayan da masu zanga-zangar suka far masa.
BBC ya ruwaito cewa, a yayin da ake ci gaba da zaman ɗar-ɗar kan abin da ka iya faruwa bayan sanar da sakamakon zaɓen Kamaru, makarantu da shaguna sun kasance a rufe a Yaoundé, babban birnin ƙasar.
Hatta ma’aikatan gwamnati da dama sun ƙi fita wuraren ayyukansu saboda fargabar abin da ka iya biyo bayan sanar da sakamakon zaɓen.
Sai dai rahotanni sun nuna cewa girke jami’an tsaro masu yawa a manyan birane, musamman Yaoundé, Douala da kuma Garoua, mahaifar jagoran adawa Tchiroma Bakary, ya taƙaita zanga-zangar da aka fara gudanarwa.
Kawo yanzu, yawancin ‘yan ƙasar sun ci gaba da kasancewa a cikin gidajensu bayan da aka bayyana Shugaba Paul Biya a matsayin wanda ya lashe zaɓen, wanda hakan ke tabbatar masa da wa’adin mulki na takwas.
Shugaba Paul Biya shi aka sanar a hukumance a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa karo na takwas a cewar Kotun Tsarin Mulkin Kamaru, yayin da tun farko jagoran ’yan adawa Issa Tchiroma Bakary ya ayyana kansa a matsayin wanda ya yi nasara.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kamaru
এছাড়াও পড়ুন:
Kamaru : Paul Biya, ya lashe zaben shugaban kasa a karo na takwas
Majalisar tsarin mulki a jamhuriyar Kamaru ta sanar da Paul Biya mai shekara 92 a matsayin wanda ya lashe zaben shugabancin kasar da aka gudanar a ranar 12 ga wata.
Mista Biya ya lashe zaben da kashi 53.66% na kuri’un da aka kada, wanda hakan ya ba shi damar shugabancin kasar a wa’adin mulki na takwas.
Saidai babban abokin hamayyarsa, Issa Tchiroma Bakary, wanda ya yi ikirarin lashe zaben, ya samu kashi 35.19% na kuri’un, a cewar alkaluman da aka samu daga cibiyar.
Madugun ‘yan adawar ya yi fatali da sakamakon zaben da ya danganta da abin dariya.
Rahotanni sun ce tarzoma ta barke a wasu sassan kasar da suka hada da Douala da Garoua bayan sanar da nasarar ta Paul Biya.
A Yaoude babban birnin kasar makarantu da shaguna sun kasance a rufe saboda fargabar abinda kan iya faruwa.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka An Nada Birgediya Janar Qarshi A Matsayin Mataimakin Babban Kwamandan Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci October 27, 2025 Hamas Ta Ce: Kungiyar Ta Ba Da ‘Yanci Ga Masu Shiga Tsakani Zabar Membobin Kwamitin Gudanar Da Gaza October 27, 2025 Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kashe ‘Yan kasar Lebanon Biyu Tare Da Jikkatan Wasu Biyu Na Daban October 27, 2025 Amnesty International Ta Bukaci Bayyana Makomar Masu Fafutukar Kare Hakkin Bil’Adama Da Suka Bace A Uganda October 27, 2025 Dakarun Kai Daukin Gaggawa Sun Yi Da’awar Kwace Karin Wasu Garuruwa A Sudan October 27, 2025 Qalibaf: Sakon Iran, Rasha da China ga MDD manuniya ce ta hadin gwiwa mai karfi October 27, 2025 Sheikh Naim: Hezbollah a shirye take ta fuskanci Isra’ila idan yaki ya barke October 27, 2025 Catherine Connolly ta lashe zaben shugaban Ireland October 27, 2025 Hamas ta sake jaddada wajabcin aiwatar da Shirin tsagaita wuta a Gaza October 27, 2025 Sudan: Dakarun sa kai na Jama’a a Arewacin Darfur sun karyata RSF kan kwace iko da El Fasher October 27, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci