More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Sabuwar dambarwa ta kunno kai tsakanin wasu manyan ‘ya’yan jam’iyyar adawa ta PDP, inda ake zargin cewa rikicin ya kai ga hana tsohon gwamnan jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, sayen fom ɗin takarar shugabancin jam’iyyar.

 

Rahotanni sun nuna cewa wasu daga cikin manyan jam’iyyar a matakin kasa sun nuna adawa da niyyar Lamido na neman kujerar shugabancin PDP, suna ganin cewa ba shi ne ya dace da wannan matsayi a yanzu ba.

Sai dai magoya bayan tsohon gwamnan sun bayyana wannan mataki a matsayin nuna son kai da kuma kokarin dakile sabuwar tafiya a cikin jam’iyyar.

NAJERIYA A YAU: Shin Ko Sauya Hafsoshin Tsaro Zai Kawo Karshen Aikin Ta’dda A Najeriya? DAGA LARABA: Shin Ko Jam’iyyar PDP Ta Fara Gushewa Ne?

Wannan lamari ya sake haska yadda PDP ke ci gaba da fama da rikicin cikin gida, wanda da yawa ke ganin zai iya shafar karfinta da hadinta kafin babban zaben da ke tafe.

Wannan shine batun da shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi duba a kai.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kabiru Tanimu Turaki

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya gana da sabbin hafsoshin tsaro

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi wata ganawar sirri da sabbin hafsoshin tsaron Najeriya a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

Sai dai babu wani cikakken bayani kan dalilin ko maudu’in wannan taron, wanda shi ne karo na farko bayan sauya manyan hafsoshin tsaron Najeriya da shugaban ƙasar ya yi.

An kashe wasu makiyaya 10 a Kebbi Zanga-zanga ta ɓarke a Kamaru

Sai dai wata majiya daga fadar shugaban kasar ta ce taron ba zai nasaba da ƙoƙarin da ake yi na ƙarfafa tsarin tsaro da inganta aikin rundunar sojoji a ƙasar nan ba.

Tinubu yayin ganawa da sabbin hafsoshin tsaro

Aminiya ta ruwaito cewa, a makon jiya ne Shugaba Tinubu ya tuɓe hafsan hafsoshin Najeriya, Janaral Christopher Musa da sauran hafsoshin tsaron ƙasar, a wani sauyi a tsarin jagorancin sojin ƙasar domin inganta da ƙarfafa sha’anin tsaro a Najeriya.

Wata sanarwa da fadar shugaban ƙasar ta fitar ta ce Tinubu ya yi musu fatan alkairi tare da bayyana sunayen sabbin hafsoshin da za su maye gurbin waɗanda aka sauke ɗin.

Sabbin hafsoshin tsaron da Tinubu ya nada sun hada da Janar Olufemi Oluyede — Hafsan Hafsoshi da Manjo Janar W Sha’aibu — Hafsan sojojin ƙasa da Air Vice Marshall S.K Aneke — Hafsan sojin sama.

Akwai kuma Rear Admiral I. Abbas — Hafsan sojin ruwa da Manjo Janar E.A.P Undiendeye — Shugaba sashen tattara bayan sirri na soji.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba
  • Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100
  • ’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi
  • Tinubu ya gana da sabbin hafsoshin tsaro
  • Ƙaddamar da Kyautar Jaruman Indomie Karo na 17: Matasan Najeriya Sun Fafata, An Samu Zakaru
  • Ƙaddamar da Kyautar Jaruman Indomie Karo Na 17 Yayin Da Zakarun Matasa Suka fafata daga karshe an samu zakaru
  • Sule Lamiɗo na neman takarar Shugaban PDP na Ƙasa
  • Tsohon Gwamnan Jigawa, Lamido Ya Bayyana Aniyar Takarar Shugabancin Jam’iyyar PDP Na Ƙasa
  • Masu yabon Buhari sun yi masa ba’a bayan ya sauka daga mulki —Gwamna Sule