Ba daidai ba ne Tinubu ya ci gaba da ciyo bashi duk da cire tallafin mai – Sanusi
Published: 29th, October 2025 GMT
Sarkin Kano kuma tsohon Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Muhammadu Sanusi II, ya bai dace gwamnatin Shugaban Kasa Bola tinubu ta ci gaba da ciyo bashi ba bayan ta cire tallafin man fetur.
Yayin da yake jawabi a Abuja ranar Talata, a taron Oxford Global Think Tank Leadership da ƙaddamar da wani littafi, Sanusi ya ce cire tallafin man ya haifar da ƙaruwar kuɗaɗen shiga na gwamnati.
Sanusi ya kuma yaba wa gwamnatin Tinubu kan cire tallafin man fetur da daidaita farashin musayar kuɗi, yana mai bayyana matakan a matsayin “masu raɗaɗi amma na wajibi.”
Sai dai ya yi gargaɗin cewa waɗannan gyare-gyare ba za su yi tasiri ba sai an haɗa su da tsari mai kyau na kashe kuɗi da gaskiya a cikin gudanar da gwamnati.
“In ka daina biyan tallafi amma ka ci gaba da yin rance, hakan na nufin ka rufe rami guda ne sai ka buɗe wani. Kalubalen da ke gabanmu yanzu shi ne ingancin yadda gwamnati ke kashe kuɗi da kuma yadda ake tafiyar da kuɗaɗen da aka ce an ajiye,” in ji shi.
Sanusi, wanda ya jagoranci CBN daga 2009 zuwa 2014, ya ce matsalolin tattalin arzikin Najeriya a yanzu sun faru ne a sakamakon rashin daidaito a manufofi da siyasar neman sai an faranta wa jama’a da aka dade ana yi.
“A shekarar 2012, mun yi gargaɗin cewa tallafin mai ba zai dore ba, amma siyasa ta shigo. Yanzu, waɗanda suka jagoranci zanga-zangar adawa da cire tallafin su ne suka gaji matsalar, kuma ba su da wani zaɓi sai su yi abin da ya dace,” in ji shi.
Ya yaba wa ƙwararrun da ke cikin tawagar tattalin arzikin gwamnati kan matakan da suka ɗauka don daidaita hauhawar farashi da rage canjin farashin kuɗi, amma ya jaddada cewa dole ne a dakile ɓarna da almubazzaranci cikin gaggawa.
Yayin da yake tambaya kan yadda gwamnati ke kashe kuɗi, Sanusi ya ce: “Me ya sa muke da ministoci 48? Me ya sa ake da jerin motocin gwamnati masu yawa? Me ya sa har yanzu ana yin rance bayan cire tallafi? In ka rufe rami guda, me ya sa za ka buɗe wani?
“Wannan gwamnati na bukatar ta duba hukumomi da yadda ake amfani da kuɗi a dukkan matakai. Domin in ka ci gaba da samun kuɗi amma kana kashewa ba daidai ba, za ka lalata duk wani ci gaba da aka samu.
“Amma irin mu da za mu ce, ‘Ya Shugaban Ƙasa, wannan ba daidai ba ne,’ ana ɗaukarmu a matsayin abokan gaba. Don haka, idan shugabanni sun kewaye kansu da masu yabon kai, ba za su taɓa samun shawara mai kyau ba.
“Shi ya sa irin su Aigboje Aig-Imoukhuede da ni kan zama kamar abokan gaba ga gwamnati, domin mutane ba sa son jin gaskiya.”
Sanusi ya ƙara da cewa: “Mun faɗa wa Buhari komai, game da buga kuɗi, almubazzaranci, farashin musayar kuɗi da tallafi, amma duk lokacin da muka yi hakan, ana ɗauka a matsayin hari kai tsaye. Waɗanda ke kewaye da shi sun sa ya ɗauke mu a matsayin abokan gaba. Shugabanni dole su fara tambaya: wa nake kewaye da kaina da su?,” in ji Sanusi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: cire rallafin mai
এছাড়াও পড়ুন:
Pezeshkian: Hadin Kai A Tsakanin Kasashen Gabas Ta Tsakiya Ba Zabi Ba Ne, Amma Dole Ne
Shugaban kasar Iran ya bayyana cewa: Haɗin kai a tsakanin kasashen yankin Gabas ta Tsakiya ba zaɓi ba ne, amma dole ne
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya jaddada cewa: Hadin kai da hadin gwiwar kasashen yankin Gabas ta Tsakiya a cikin tsarin Kungiyar Hadin Kan Tattalin Arziki (ECO) ba wani zaɓi ne na siyasa ba, a’a, wani muhimmin abu ne don cimma ci gaba, tsaro, da kwanciyar hankali a yankin.
A lokacin jawabinsa a taron Ministocin harkokin cikin gida na kasashe membobin ECO na hudu, Pezeshkian ya lura cewa: Kiran wannan taron bayan dogon hutu yana nuna sha’awar kasashen membobinta na inganta hadin kai da hadin gwiwa a muhimman fannoni da ke shafar dangantakar yankuna. Ya bayyana cewa ma’aikatun cikin gida muhimman ma’aikatu ne, domin, ban da nauyin da ke kansu na musamman, suna da alhakin samar da kayayyakin more rayuwa don ci gaban tattalin arziki da kuma tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a cikin kasashen membobin.
Shugaban kasar ta Iran ya kara da cewa: Nasarar hadin gwiwar tattalin arziki na yankuna yana bukatar tsarin hadin gwiwa mai karfi, mai dorewa, wanda ake iya hasashensa, da kuma juriya, yana mai nuna muhimmiyar rawar da ma’aikatun cikin gida ke takawa wajen hada wadannan tushe.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Mataimakin Ministan Harkokin Waje Kan Harkokin Siyasa Na Iran Ya Ce: Iran Ba Ta Kula Da Matsin Lamba October 28, 2025 Baqa’i: Dokar Majalisar Shawarar Musulunci Ce Ke Jagorantar Hadin Kan Iran Da Hukumar IAEA October 28, 2025 Sojojin Isra’ila Sun Kai Hare-Hare Kan Yankin Gaza A Matsayin Karya Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta October 28, 2025 Al-Burhan: Sojojin Sudan Sun Janye Daga El-Fasher Saboda Kare Rayukan Fararen Hula October 28, 2025 Baqaei: Iran ta daɗe tana aiki don haɓaka zaman lafiya a duniya October 28, 2025 An Yi Girgizar Kasa Mai Karfi A Kasar Turkiya October 28, 2025 Ouattara Na Kasar Ivory Coast Ya Lashe Zaben Shugaban Kasa October 28, 2025 MDD Ta Yi Kira Da Abude Kafar Shigar Da Kayan Agaji Zuwa Garin El-Fashar October 28, 2025 Wilayati: Kasashen Ian, China Da Rasha Suna Taka Rawa A Fagen Kafa Sabon Tsarin Duniya October 28, 2025 Zaben Ivory Coast: Alassane Ouattara na kan gaba da tazara mai yawa October 27, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci