Shima da yake jawabi a wajen taron, kwamishinan harkokin mata, yara da nakasassu na jihar Kano, wanda daraktan gudanarwa, Alhaji Mohammed Sambo Iliyasu ya wakilta, ya jaddada goyon bayan jihar kan ci gaban harkokin inganta zamantakewa da walwalar al’umma.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku.

Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara Ta Taya Oluremi Tinubu Murnar Nadin Sarauta a Ile-Ife

Daga Aminu Dalhatu

Uwargidar Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta taya Uwargidar Shugaban Kasa, Sanata Oluremi Tinubu, murna bisa nadin ta a matsayin Yeye Asiwaju Gbogbo Ile Oodua a Ile-Ife na  Jihar Osun.

Nadin ya kasance wani bangare na bukukuwan cikar shekaru 10 na Mai Martaba Ooni Adeyeye Enitan Ogunwusi Ojaja II akan karagar mulki na Ooni Ife, wanda ya jawo sarakunan gargajiya, manyan jami’an gwamnati da fitattun mutane daga sassan kasar nan.

A wata sanarwa da sakatariyar yada Labarai ta Uwargidar Gwamnan, Rabi Yusuf, ta fitar, ta bayyana karramawar da aka yi wa Sanata Oluremi a matsayin abin yabawa, inda ta ce karramawar ta yi daidai da jajircewarta wajen ci gaban kasa, tallafawa mata, da kuma gudummawarta wajen karfafa iyalai da al’umma ta hanyar aikace-aikacen jin kai da manufofin raya al’umma.

Ta kuma yaba wa Ooni na Ife bisa zabar Sanata Oluremi Tinubu domin wannan girmamawa, tana mai cewa wannan zabe ya nuna irin jagoranci, tasiri da dogon lokacin da ta shafe tana hidima ga kasa.

A cewar Hajiya Huriyya, wannan zabe ya nuna rawar da masarautu ke takawa wajen gane karrama wadanda suka yi wa al’umma  hidima.

Bikin ya nuna al’adun Yarbawa da kuma muhimmancin gudunmawar da masarautu ke bayarwa wajen gina hadin kan kasa.

Manyan shugabannin gargajiya da suka halarci bikin sun hada da Sarkin Musulmi, Olu na Warri, da Soun na Ogbomoso, da sauransu, wadanda suka hadu domin bikin cikar Ooni shekaru 10 a kan karaga da kuma nadin Sanata Oluremi Tinubu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Kara Samar da Shirye-shiryen Inganta Rayuwar Masu Buƙata ta Musamman
  • NAFDAC ta lalata kayayyakin Naira biliyan 5 a Jihar Nasarawa
  • Manchester United ta shiga zawarcin Sergio Ramos
  • Gwamnan Kano ya naɗa mace ta farko a matsayin shugabar Jami’ar Northwest
  • Ma’aikatar Mata da Walwalar Jama’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudinta a Gaban Majalisa
  • Ba ni da shirin ficewa daga PDP — Gwamnan Bauchi
  • Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara Ta Taya Oluremi Tinubu Murnar Nadin Sarauta a Ile-Ife
  • Iran Tana Daukar Bakwancin Taron BRICS Na Binciken Kimiya Da Kuma Ci Gaban Ilmi
  • Gwamnan Jihar Ribas ya sauya sheka zuwa APC
  • ASUU-SSU Ta Zargi VC Da KaryDokokin Jami’ar Jihar Sakkwato