Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Taron Ƙarawa Ma’aikatan Jinƙai Sani A Jihar Kano
Published: 17th, April 2025 GMT
Shima da yake jawabi a wajen taron, kwamishinan harkokin mata, yara da nakasassu na jihar Kano, wanda daraktan gudanarwa, Alhaji Mohammed Sambo Iliyasu ya wakilta, ya jaddada goyon bayan jihar kan ci gaban harkokin inganta zamantakewa da walwalar al’umma.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku.
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Katsina Ta Umurci a Gaggauta Rufe Dukkan Makarantun Jihar
Daga Isma’il Adamu
Gwamnatin Jihar Katsina ta umarci gaggauta rufe dukkan makarantun gwamnati, da na masu zaman kansu a fadin jihar biyo bayan kalubalen tsaro da ya addabi makarantun kasar nan.
Wannan mataki na zuwa ne bayan wasu hare-haren sace ɗaliban makarantu da suka faru a jihohin Kebbi da Neja kwanan nan.
Wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na Ma’aikatar Ilimin Firamare da Sakandare, Sani Danjuma, ya sanyawa hannu, ta ce an ɗauki wannan mataki ne domin nuna jajircewar gwamnati wajen kare ɗalibai, malamai da ma’aikatan makarantu.
Sanarwar ta ce duk da cewa rufe makarantun na iya kawo cikas ga iyaye da ɗalibai, tsaro ya fi komai muhimmanci yayin da hukumomi ke ci gaba da ƙarfafa matakan tsaro a makarantu.
Ta kuma bukaci hukumomin makarantu da su tabbatar da bin umarnin, tare da kiran iyaye da su ba da haɗin kai, a yayin da gwamnati tare da hukumomin tsaro ke ci gaba da sa ido kan al’amuran domin yiwuwar sake duba wannan mataki.