‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara
Published: 30th, October 2025 GMT
ShareTweetSendShare MASU ALAKA  Labarai Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai October 30, 2025 
 Manyan Labarai Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda  October 30, 2025 
 Manyan Labarai Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC October 30, 2025 
এছাড়াও পড়ুন:
Sassauci na yi wa Maryam Sanda ba afuwa ba — Tinubu
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi sassauci wa matar nan da kotu ta yankewa hukuncin kisa bayan samunta da laifin kashe mijinta, Maryam Sanda.
Wannan dai na zuwa ne bayan shugaban kasar ya janye sunan Maryam Sanda daga cikin jerin waɗanda ya yi wa afuwa a kwanakin baya.
Super Falcons ta samu gurbin buga Kofin Afrika An kashe mutum 2 a rikicin limancin masallacin Juma’a a TarabaAna iya tuna cewa, a farkon watan Oktoba nan ne dai shugaba Tinubu ya yi wa wasu mutum 175 afuwa da suka haɗa da matattu da masu rayayyu.
Abin da ya fi daukar hankali a lokacin da aka sanar da afuwar shi ne ganin sunayen mutanen da suka aikata manyan laifuka, cikin wadanda aka yafewa, musamman manyan masu ta’ammali da fataucim miyagun kwayoyi, da masu kisan kai, da masu garkuwa da mutane, da masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba, da gaggan masu cin hanci da rashawa.
Sai dai sanarwar da mai magana da yawun shugaban kasar Bayo Onanuga ya fitar a ranar Laraba ta ce bayan tuntuba da tattaunawa da Majalisar Magabata ta Kasa da jin ta ra’ayoyin mutane a kan lamarin, Shugaba Tinubu ya ba da umarnin sake nazarin jerin sunayen mutanen da aka yi wa afuwar karkashin dokar da ta ba shi iko ta sashe na 175 (1) da (2) ta Kundin Tsarin Mulkin 1999.
Sabon jerin sunayen mutanen ya ƙunshi mutum 116, inda aka kasa su gida uku — waɗanda aka yi wa afuwa da waɗanda aka yi wa sassauci da kuma waɗanda aka yi afuwa amma ba a wanke su ba.
Mutum 50 shugaban ya cire sunayensu daga cikin waɗanda ya yi wa afuwar, ciki har da Maryam Sanda.
Sanarwar ta ambato cewa Maryam Sanda za ta ci gaba da zaman gidan yari har na tsawon shekaru shida nan gaba—jimilla shekaru 12 ke nan — maimakon ta fuskanci hukuncin kisan da aka yanke mata tun farko.
Maryam wadda aka ɗaure a shekarar 2020 yanzu haka ta yi shekaru shida, inda ake sa ran nan da shekaru shida za ta shaƙi iskar ’yanci.
Jerin sunayen ciki har da Maryam Sanda ya ƙunshi mutum 86 da aka sassautawa hukuncin da aka yanke musu, inda masu hukuncin kisa ya koma ɗaurin rai da rai sannan wasu kuma aka rage musu yawan shekarun da za su yi a gidan wakafi.
 UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba
UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba