Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta
Published: 27th, October 2025 GMT
A yau Litinin 27 ga Oktoba, kungiyar jigilar kayayyaki da sayayya ta kasar Sin ta ba da rahoton bayanan ayyukan jigilar kayayyakin dake bukatar kankara a watannin Yuni da Yuli da Agustan bana. Bayanan na nuna cewa, a karkashin jagorar manufofi da bukatun kasuwa, aikin jigilar kayayyakin dake bukatar kankara ya nuna samun ci gaba mai karfi tare da fadada girman kasuwa.
Bayanan sun nuna cewa, jimillar da aka samu a wannan bangare a wadannan watanni 3 ta kai tan miliyan 117.3, wadda ta karu da kashi 4.72% idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata. A cikin watanni 3 na farko na wannan shekara, jimillar jigilar abincin dake bukatar kankara ta kai tan miliyan 309.3, wadda ta karu da kashi 4.49%.
Dangane da kudaden shiga, jimillar kudaden shiga na kamfanonin gudanar da ayyukan jigilar abincin dake bukatar kankara a watannin Yuni da Yuli da Agusta ta kai Yuan biliyan 144.97, wato ta zarce dala biliyan 20, wadda ta karu da kashi kashi 3.92%. A cikin watanni 9 na farko na wannan shekara, jimillar kudaden shiga na wadannan kamfanoni ta kai Yuan biliyan 424.91, kwatankwacin abin da ya haura dala biliyan 59 , wanda ya karu da kashi 3.85%. (Amina Xu)
ShareTweetSendShare MASU ALAKAকীওয়ার্ড: dake bukatar kankara karu da kashi
এছাড়াও পড়ুন:
Shirin Soil Values Da NAIDA Sun Fito Da Tsarin Saukaka Samun Kayayyakin Gona Ga Manoma
Shirin Inganta Noma da Kula da Sauyin Yanayi na Soil Values, tare da haɗin gwiwar Kungiyar Dillalan Kayayyakin Aikin Gona ta Kasa (NAIDA) ta Arewa maso Yamma, ya ƙaddamar da sabon tsari domin sauƙaƙa samun kayayyakin gona ga ƙananan manoma a yankunan Arewacin Najeriya, da ake kira “one-stop shop a turance.
Jami’ar shirin ta kasa Misis Medina Ayuba Fagbemi, ta bayyana cewa za a samar da shagunan tafi-da-gidanka guda tara da za su kai kayayyaki zuwa sama da al’ummomi 20 a jihohin Kano, Jigawa da Bauchi, inda ake sa ran shirin zai amfanar da kusan ƙananan manoma 7,000.
Ta ce tsarin zai taimaka wajen kusantar da ingantattun iri, taki da magungunan kashe kwari ga manoma, tare da samar da shawarwari na gona, gwajin ƙasa da kuma tantance bayanan manoma ta yanar gizo.
Misis Medinat Fagbemi ta yaba wa manoma da malaman gona da suka amince da wannan tsari, tana ƙarfafa su da su yi aiki da gaskiya da tare da jajircewa.
A nasa jawabin, Mataimakin Shugaban kungiyar NAIDA Arewa maso Yamma, Injiniya Abdullahi Muhammad, ya shawarci wadanda suka ci gajiyar shirin da su aiwatar da horon da suka samu yadda ya kamata, yayin da Daraktan Hukumar Sauya Fasalin Noma ta Jigawa, Dr. Saifullahi Umar, ya tabbatar da goyon bayan gwamnatin jihar domin cimma nasarar shirin.
Shirin Soil Values, wanda gwamnatin kasar Netherlands ke tallafawa da Yuro Miliyan 100 na tsawon shekaru goma, an kirkiro sa ne da nufin farfaɗo da ƙasar noma, rage gibin amfanin gona, da farfado da ƙasar da ta lalace a Najeriya da wasu ƙasashen Yammacin Afirka.
Usman Muhammad Zaria