Shugaban karamar hukumar Gwarzo, Dr. Mani Tsoho, ya yi gargaɗi ga mazauna yankin kan mummunan ɗabi’ar shan magani ba tare da shawarar likita ba, yana mai bayyana hakan a matsayin babban haɗari ga lafiya da ka iya janyo matsalolin da ke barazana ga rai.

Dr. Tsoho ya yi wannan gargaɗi ne yayin da yake ziyarar duba asibitin Gwarzo General Hospital, inda ya gana da marasa lafiya, ya duba yadda ake gudanar da ayyuka, tare da yabawa ma’aikatan lafiya bisa jajircewarsu wajen kula da jama’a.

Ya nuna damuwa cewa, yawancin matsalolin lafiya da ake fuskanta a cikin al’umma na faruwa ne sakamakon amfani ko wuce gona da iri wajen shan magunguna ba tare da shawarwarin ƙwararru ba.

Ya shawarci jama’a da su nemi shawarar likitoci da masu magunguna kafin su sha kowanne irin magani.

Shugaban karamar hukumar ya yi kira ga mazauna yankin da su rika ziyarar asibiti mafi kusa da zarar sun ji wata alamar rashin lafiya don samun kulawa cikin lokaci.

Ya tabbatar da cewa akwai likitoci da nas-nas ƙwararru a cibiyoyin lafiya na yankin da za su samar da ingantacciya kulawa.

Yayin da yake jaddada kudirin gwamnatinsa na inganta harkokin lafiya a dukkan yankuna, Dr. Tsoho ya ce hukumar tana aiki don samar da isassun magunguna, kayan aiki na zamani da kuma horaswa ga ma’aikatan lafiya.

Baya ga batun lafiya, shugaban ya kuma yi kira ga jama’a da su kasance masu lura da tsaro, tare da yin gaggawar kai rahoton duk wani motsi ko mutum da ba su yarda da shi ba ga jami’an tsaro domin daukar mataki cikin lokaci.

 

Daga Khadijah Aliyu

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Miyagun Kwayoyi

এছাড়াও পড়ুন:

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Kakakin rundunar ‘yansandan jihar Gombe, DSP Buhari Abdullahi, ya shaida wa LEADERSHIP cewa, wasu manoma uku da makiyayi daya sun samu kananan raunuka. Ya kara da cewa an tura ‘yansanda da ‘yan banga na yankin don dawo da zaman lafiya.

 

Kakakin rundunar ‘yansandan ya kuma ce, sun kama mutane 17 da ake zargi da hannu a rikicin, amma zaman lafiya da kwanciyar hankali ya dawo a yankin.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260 October 28, 2025 Labarai Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi October 28, 2025 Manyan Labarai Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba October 28, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jihar Jigawa Ce Ta Fara Biyan Kudaden Kujerun Aikin Hajjin 2026- NAHCON
  • Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro
  • Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba
  • Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe
  • Jami’an tsaro sun harbi matar aure sun lakaɗa wa jama’a duka a Katsina 
  • Baqa’i: Dokar Majalisar Shawarar Musulunci Ce Ke Jagorantar Hadin Kan Iran Da Hukumar IAEA
  • Jami’an tsaro sun kashe ’yan bindiga 80 a Kebbi
  • Baqaei: Iran ta daɗe tana aiki don haɓaka zaman lafiya a duniya
  • Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana