AA Zaura Ya Yi Kira Ga ’Yan Nijeriya Su Marawa Sauye-sauyen Shugaba Tinubu Baya
Published: 29th, October 2025 GMT
Daya daga cikin manyan jiga-jigan jam’iyyar All Progressives Congress (APC) kuma ɗan kasuwa mai taimakon al’umma, Abdussalam Abdulkarim Zaura, wanda aka fi sani da AA Zaura, ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su ba da cikakken goyon bayansu ga gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, yana mai bayyana kwarin gwiwa cewa shugaban na da kwarewa da hangen nesa wajen farfado da tattalin arzikin ƙasar da inganta jin daɗin jama’a.
Zaura ya yi wannan kiran ne lokacin da wata tawaga daga Tinubu/Shettima Campaign Group ta kai masa ziyarar ban girma a ofishinsa, inda ya jaddada cewa haɗin kan ’yan Nijeriya na da matuƙar muhimmanci domin samar da ci gaba mai ɗorewa da kuma tabbatar da matsayi irin na ƙasashen da ke da ƙarfafa tattalin arziki da ingantaccen rayuwa.
“Ina kira ga ’yan Nijeriya da su marawa Shugaba Bola Ahmed Tinubu baya domin ya ja-goranci Nijeriya zuwa sahun ƙasashen da ke da ƙarfi a tattalin arziki da kuma sauƙin rayuwa a duniya,” in ji Zaura.
Jigon na APC, wanda ya shahara wajen ayyukan taimako da shirye-shiryen ƙarfafa matasa, ya ce sauye-sauyen tattalin arzikin da Shugaba Tinubu ke aiwatarwa yanzu, duk da cewa suna da kalubale a farkon lokaci, suna da nufin gina tattalin arzikin ƙasar ne bisa tubalin ƙirƙira, gaskiya da ɗorewar ci gaba.
Ya ce matakan da gwamnati ta ɗauka, irin su cire tallafin man fetur da sake fasalin harkar musayar kuɗi (forex reform), muhimman matakai ne da za su taimaka wajen gyara matsalolin tsari da aka dade da fama da su, tare da shirya ƙasar don samun bunƙasar tattalin arziki a nan gaba.
“Duk wata babbar ƙasa ta fuskanci lokacin sauye-sauye kafin ta kai matsayin da ta samu kwanciyar hankali da ci gaba. Abin da ake buƙata a yanzu shi ne haƙuri, haɗin kai da amincewa da hangen nesan gwamnati,” in ji shi.
Zaura ya kuma shawarci shugabannin siyasa, kungiyoyin farar hula da masu zaman kansu da su haɗa kai da gwamnati wajen aiwatar da shirinta na ci gaba maimakon siyasantar da kalubalen da ke tattare da sauye-sauyen.
A cewarsa, gwamnatin Tinubu ta mayar da hankali ne wajen ƙirƙirar ayyukan yi, bunƙasa noma, ƙarfafa kirkire-kirkiren fasaha (digital innovation), da kuma zuba jari a fannin gine-gine da ababen more rayuwa, a matsayin dabarar rage talauci da ƙarfafa tattalin arzikin jama’a, musamman matasa da mata.
Ya ƙara da cewa ’yan Nijeriya su ci gaba da kasancewa masu ƙwarin guiwa da juriya, yana mai bayyana cewa shirin gwamnati na sake fasalin tattalin arziki zai fara haifar da sakamako mai gamsarwa nan ba da jimawa ba.
Zaura ya sake jaddada goyon bayansa ga gwamnatin APC, yana bayyana Shugaba Tinubu a matsayin jagora mai hangen nesa da ƙarfin gwiwa wajen ɗaukar matakan da za su dawo da ƙasar kan turbar ci gaba.
“Jagoranci ba na jin daɗi ba ne, amma na ƙarfin hali — ƙarfin hali na ɗaukar matakai masu wahala don amfanin jama’a na dogon lokaci. Ina da tabbacin Shugaba Tinubu yana da wannan ƙarfin hali, kuma da goyon bayanmu, Nijeriya za ta fi ƙarfafa,” in ji shi.
Ya kuma jaddada aniyar sa ta ci gaba da tallafawa ƙoƙarin gwamnati ta hanyar aikin sa na gidauniyar taimako, wadda ke aiwatar da shirye-shirye a fannin ilimi, kasuwancin zamani (digital entrepreneurship) da ƙarfafa matasa, wanda ya bayyana a matsayin ginshiƙi wajen gina ƙasa mai ɗorewa da dogaro da kai.
Zaura ya kuma yi kira ga ’yan Nijeriya daga kowane bangare da su fifita zaman lafiya, haɗin kan ƙasa da tattaunawa mai ma’ana wajen shawo kan matsalolin tattalin arziki da zamantakewa.
“Mu daina kallon bambance-bambance, mu haɗa kai don cigaban ƙasarmu mai albarka. Nijeriya tana da cikakken damar zama ƙasa mai girma, kuma ƙarƙashin jagorancin Shugaba Tinubu, wannan mafarki zai tabbata,” in ji Zaura.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: a tattalin arziki tattalin arzikin yan Nijeriya
এছাড়াও পড়ুন:
Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya
A kwanan nan, wata manufa da aka zartas a yayin wani taron kwamitin tsakiya na jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, ta janyo hankalin al’ummun duniya, wato yadda kasar Sin take neman gaggauta dogaro da kai wajen kirkiro sabbin fasahohi, da zama mai jagorantar ci gaban masana’antun zamani a duniya. Inda dimbin kafofin yada labaru na kasashe daban daban ke ganin cewa, manufar ta nuna muhimmancin da kasar Sin ta dora a bangaren raya kasa ta wata ingantacciyar hanya, da bunkasa fannin kimiyya da fasaha, wadda ita ma ta zame wa sauran kasashe abin koya.
Hakika, a wannan zamani da muke ciki, kusan dukkan kasashe suna sa lura kan aikin raya sabbin masana’antu. Saboda ra’ayi na kariyar cinikayya ya haifar da cikas ga tsarin dunkulewar tattalin arzikin duniya, da yunkuri na samun farfadowa a fannin saurin ci gaban tattalin arziki, lamarin da ya sanya kasashe daban daban ke kokarin neman sabbin sana’o’in da za su sa kaimi ga karuwar tattalin arzikinsu. Kana a bangaren kasar Sin, yawan kamfanoninta masu sarrafa sabbin fasahohi ya riga ya zarce dubu 500, yayin da adadin manyan rukunonin kirkiro sabbin fasahohin zamani a kasar, wadanda ke cikin jerin sunayen rukunoni mafi girma guda 100 na duniya, ya kai 26. Wadannan misalai sun shaida yadda kasar take dogaro kan ci gaban fasahohi wajen raya tattalin arziki.
Bisa shirin da aka zartas a taron kwamitin tsakiya na jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin na wannan karo, Sin za ta kara kokarin samar da sabbin fasahohi masu muhimmanci, da hada bangaren kirkiro fasahohi da na sabunta masana’antu waje guda, da raya aikin ilimi a kokarin samar da kwararru masu nazarin kimiyya da fasaha, da dai makamantansu. Hakan ya nuna yadda kasar ke neman raya kai ta wasu ingantattun dabaru, tare da sa kaimi ga ci gaban tattalin arzikin duniya, da raba damammaki na samun ci gaba tare da sauran kasashe. (Bello Wang)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA