Aminiya:
2025-12-14@03:36:35 GMT

AA Zaura Ya Yi Kira Ga ’Yan Nijeriya Su Marawa Sauye-sauyen Shugaba Tinubu Baya

Published: 29th, October 2025 GMT

Daya daga cikin manyan jiga-jigan jam’iyyar All Progressives Congress (APC) kuma ɗan kasuwa mai taimakon al’umma, Abdussalam Abdulkarim Zaura, wanda aka fi sani da AA Zaura, ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su ba da cikakken goyon bayansu ga gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, yana mai bayyana kwarin gwiwa cewa shugaban na da kwarewa da hangen nesa wajen farfado da tattalin arzikin ƙasar da inganta jin daɗin jama’a.

Zaura ya yi wannan kiran ne lokacin da wata tawaga daga Tinubu/Shettima Campaign Group ta kai masa ziyarar ban girma a ofishinsa, inda ya jaddada cewa haɗin kan ’yan Nijeriya na da matuƙar muhimmanci domin samar da ci gaba mai ɗorewa da kuma tabbatar da matsayi irin na ƙasashen da ke da ƙarfafa tattalin arziki da ingantaccen rayuwa.

“Ina kira ga ’yan Nijeriya da su marawa Shugaba Bola Ahmed Tinubu baya domin ya ja-goranci Nijeriya zuwa sahun ƙasashen da ke da ƙarfi a tattalin arziki da kuma sauƙin rayuwa a duniya,” in ji Zaura.

Jigon na APC, wanda ya shahara wajen ayyukan taimako da shirye-shiryen ƙarfafa matasa, ya ce sauye-sauyen tattalin arzikin da Shugaba Tinubu ke aiwatarwa yanzu, duk da cewa suna da kalubale a farkon lokaci, suna da nufin gina tattalin arzikin ƙasar ne bisa tubalin ƙirƙira, gaskiya da ɗorewar ci gaba.

Ya ce matakan da gwamnati ta ɗauka, irin su cire tallafin man fetur da sake fasalin harkar musayar kuɗi (forex reform), muhimman matakai ne da za su taimaka wajen gyara matsalolin tsari da aka dade da fama da su, tare da shirya ƙasar don samun bunƙasar tattalin arziki a nan gaba.

“Duk wata babbar ƙasa ta fuskanci lokacin sauye-sauye kafin ta kai matsayin da ta samu kwanciyar hankali da ci gaba. Abin da ake buƙata a yanzu shi ne haƙuri, haɗin kai da amincewa da hangen nesan gwamnati,” in ji shi.

Zaura ya kuma shawarci shugabannin siyasa, kungiyoyin farar hula da masu zaman kansu da su haɗa kai da gwamnati wajen aiwatar da shirinta na ci gaba maimakon siyasantar da kalubalen da ke tattare da sauye-sauyen.

A cewarsa, gwamnatin Tinubu ta mayar da hankali ne wajen ƙirƙirar ayyukan yi, bunƙasa noma, ƙarfafa kirkire-kirkiren fasaha (digital innovation), da kuma zuba jari a fannin gine-gine da ababen more rayuwa, a matsayin dabarar rage talauci da ƙarfafa tattalin arzikin jama’a, musamman matasa da mata.

Ya ƙara da cewa ’yan Nijeriya su ci gaba da kasancewa masu ƙwarin guiwa da juriya, yana mai bayyana cewa shirin gwamnati na sake fasalin tattalin arziki zai fara haifar da sakamako mai gamsarwa nan ba da jimawa ba.

Zaura ya sake jaddada goyon bayansa ga gwamnatin APC, yana bayyana Shugaba Tinubu a matsayin jagora mai hangen nesa da ƙarfin gwiwa wajen ɗaukar matakan da za su dawo da ƙasar kan turbar ci gaba.

“Jagoranci ba na jin daɗi ba ne, amma na ƙarfin hali — ƙarfin hali na ɗaukar matakai masu wahala don amfanin jama’a na dogon lokaci. Ina da tabbacin Shugaba Tinubu yana da wannan ƙarfin hali, kuma da goyon bayanmu, Nijeriya za ta fi ƙarfafa,” in ji shi.

Ya kuma jaddada aniyar sa ta ci gaba da tallafawa ƙoƙarin gwamnati ta hanyar aikin sa na gidauniyar taimako, wadda ke aiwatar da shirye-shirye a fannin ilimi, kasuwancin zamani (digital entrepreneurship) da ƙarfafa matasa, wanda ya bayyana a matsayin ginshiƙi wajen gina ƙasa mai ɗorewa da dogaro da kai.

Zaura ya kuma yi kira ga ’yan Nijeriya daga kowane bangare da su fifita zaman lafiya, haɗin kan ƙasa da tattaunawa mai ma’ana wajen shawo kan matsalolin tattalin arziki da zamantakewa.

“Mu daina kallon bambance-bambance, mu haɗa kai don cigaban ƙasarmu mai albarka. Nijeriya tana da cikakken damar zama ƙasa mai girma, kuma ƙarƙashin jagorancin Shugaba Tinubu, wannan mafarki zai tabbata,” in ji Zaura.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: a tattalin arziki tattalin arzikin yan Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Kano ya naɗa mace ta farko a matsayin shugabar Jami’ar Northwest

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da naɗin Farfesa Amina Salihi Bayero, a matsayin sabuwar Shugabar Jami’ar Northwest.

Naɗin nata zai fara aiki daga ranar 1 ga watan Disamban 2025, har zuwa tsawon shekaru biyar.

EFCC ta tsare tsohon ministan ƙwadago, Chris Ngige An koro ’yan Najeriya 32 kan kasuwancin miyagun ƙwayoyi a Indiya

Mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ne, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis.

Sanarwar, ta ce gwamnan ya amince da naɗin ne bayan  tantancewa da kwamitin gudanarwar jami’ar ya yi mata.

A matsayinsa na jagoran jami’ar, Gwamna Abba, ya yaba wa shugaban kwamitin da mambobinsa kan jajircewarsu wajen bin ƙa’idojin tantancewar.

Haka kuma ya nemi a yi mata addu’ar samun nasara wajen gudanar da jagorancin Jami’ar.

Farfesa Amina Salihi Bayero ƙwararriya ce a fannin Chemistry, musamman Analytical Chemistry, kuma ita ce mace ta farko da ta samu digiri na uku a fannin daga Jami’ar Bayero Kano.

Ta taɓa riƙe muƙamai da dama a harkar ilimi da gudanarwa, ciki har da shugabar sashen Chemistry, da kuma Mataimakiyar Shugabar Jami’a (DVC) a Jami’ar Yusuf Maitama Sule.

Ana girmama ta saboda jajircewarta wajen horar da matasan masana kimiyya.

Ana sa ran naɗin nata zai ƙara ɗaukaka martabar jami’ar, ya inganta tsarin ilimi, tare da bai wa mata ƙofar samun manyan muƙamai a Jihar Kano.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Karatun Baya Dangane Da Tarihi Shi Ne Abun Da Ya Kamaci Japan
  • Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Samar Da Damammakin Raya Tattalin Arziki Ga Duniya A Shekara Mai Zuwa
  • Shugaba Tinubu Ya Karrama Shugaban NPA Da Lambar Yabo Ta Musamman
  • ’Yan sanda sun ba da tabbacin isasshen tsaro a zaɓen ƙananan hukumomin Borno
  • Tinubu Ya Yaba Wa Jami’an Tsaro Kan Ceto Dalibai 100 Da Aka Sace A Neja
  • Kotun Koli ta soke afuwar da Tinubu ya yi wa Maryam Sanda
  • Taron Abuja kan Tattaunawakan Tattalin Arziki Kasa- “Akwai yiyuwar tattalin arzikin kasa zai murmure a shekarar 2026”
  • Nazarin CGTN: Fahimtar Matsayin Sin Cikin Yanayin Tattalin Arzikin Duniya Na Da Muhimmanci
  • Manchester United ta shiga zawarcin Sergio Ramos
  • Gwamnan Kano ya naɗa mace ta farko a matsayin shugabar Jami’ar Northwest