Aminiya:
2025-10-29@00:02:13 GMT

Netanyahu ya ba da umarnin kai mummunan farmaki a Gaza

Published: 28th, October 2025 GMT

Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya umarci rundunar sojin ƙasar da ta kai mummunan farmaki a Zirin Gaza, bayan ya zargi ƙungiyar Hamas da karya yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma.

Wata sanarwa da ofishin firaministan ya fitar, ta ce: “Bayan tattaunawar tsaro, Firaminista Netanyahu ya umurci rundunar soji da ta gaggauta kai hare-hare masu ƙarfi a Zirin Gaza.

Juventus ta kori kocinta Igor Tudor An raba wa iyalan ’yan sandan da suka mutu tallafin N31m a Jigawa

Sanarwar na zuwa ne bayan Isra’ila ta zargi Hamas ta karya sharuɗɗan yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma kwanakin baya domin ba da damar kai agaji ga fararen hula da ke yankin.

Tun da farko dai Netanyahu ya sha alwashin mayar da martani kan abin da ya kira saɓa yarjejeniyar tsagaita wuta, inda ya ce Hamas ta gaza tabbatar da sharuɗɗan yarjejeniyar da suka haɗa da miƙa dukkan mutanen da ta yi garkuwa da su waɗanda suka haɗa rayayyu da matattu.

Duk da gwamnatin Isra’ila ta tabbatar da cewa ƙungiyar Hamas ta miƙa waɗanda suka raye, amma har yanzu ba ta ƙarasa miƙa gawarwakin matattun ba, abin da ya janyo zargin cewa tana ƙoƙarin saɓa yarjejeniyar.

A nata ɓangaren kuwa, Hamas ta bayyana cewa nemo gawarwakin na da wahalar gaske ne, saboda baraguzan gine-ginen da Isra’ila ta rusa da ke kawo cikas wajen lalubo gawarwakin.

A bayan nan ne Isra’ila ta tabbatar da cewa gawar mutumin da Hamas ta miƙa mata a ranar Litinin ba ta cikin gawarwakin da ƙungiyar ta yi garkuwa da su da aka tsara za ta mayar da su.

Har yanzu dai ana neman gawarwaki 13 daga cikin waɗanda Hamas ta yi garkuwa da su, waɗanda ake tunanin za ta miƙa domin cika sharuɗan yarjejeniyar tsagaita wuta da Shugaba Trump ya tsara domin kawo ƙarshen yaƙin Gaza.

Hukumomin Isra’ila sun ɗauki hakan a matsayin yunƙurin Hamas na karya alƙawarin da aka shiga domin kawo ƙarshen yaƙin.

Mun jinkirta miƙa gawa a yau Talata —Hamas

Ƙungiyar Hamas ta sanar da cewa ta jinkirta miƙa gawar wani wanda aka tsara za ta miƙa da yammacin Talatar nan, saboda abin da ta kira saƙonin karya yarjejeniyar tsagaita wuta da Isra’ila ta yi.

A sanarwar da sashen yaƙin ƙungiyar, Ezzedine Al-Qassam Brigades, suka fitar, ƙungiyar ta ce ta ɗauki wannan mataki ne sakamakon abin da ta bayyana a matsayin “saɓa yarjejeniyar tsagaita tsagaita wuta da Amurka ta shiga tsakani wajen tsara ta.”

“Za mu jinkirta miƙa gawar da aka tsara a yau [Talata] saboda take haƙƙin da Isra’ila ta yi.

Duk wani sabon farmaki daga Isra’ila zai iya kawo cikas wajen aikin bincike, tono, da ceto gawarwakin,” in ji sanarwar.

Sanarwar ta fito ne ‘yan mintuna kaɗan bayan Firaminista Netanyahu ya umurci sojojinsa da su kai mummunan farmaki a Zirin Gaza, yana zargin Hamas da karya sharuɗɗan yarjejeniyar tsagaita wuta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Benjamin Netanyahu Falasɗinawa yarjejeniyar tsagaita wuta da Netanyahu ya Isra ila ta

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Ki Zuwa Taron Sherme-Sheikh Ne Saboda Kar Ta Zama  Mai Shaidar Zur Akan Kisan Kiyashin Gaza

Babban sakataren Majalisar koli ta tsaron kasar Iran  Ali Larijani ya bayyana cewa; Bayan da aka dauki shekaru biyu ana yi wa mutanen Gaza kisan kiyashi, wanda mutane 70,000 su ka yi shahada, wasu fiye da 100,000 su ka jikkata, suna son a rufe wannan laifin da taron zaman lafiya.

Ali Larijani ya kara da cewa; Sun kashe al’ummar Falasdinu, sun hana shi abinci da ruwa, yanzu kuma suna son bayyana kawukansu a matsayin masu ceto da Falasdinawa, don haka wannan taron ba komai ba ne sai wasan kwaikwaiyo.

Taron da aka yi a Sherm-Sheikh na Masar an yi shi ne a karkashin jagorancin shugaban Amurka Donald Trump wanda kasarsa ce ta kasance a gaba wajen bayar da makamai ga HKI a tsawon lokacin yaki.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Jami’ar ABU Ta Karyata Zargin Da Ake yi Na Kera Makamin Nukiliya A Asirce October 25, 2025 M D D Ta ce Akalla Mutane miliyan 1.5 Ne Ke Bukatar Taimakon Gaggawa A Gaza October 25, 2025 Tony Balai Na Fuskantar Turjiyar Kasashen Larabawa Game Da Rawar Da Zai Taka A Gaza. October 25, 2025 Yau Ne Ake Gudanar Da Zaben Shugaban Kasa  A Ivory Coast October 25, 2025 Iran Za ta Karbi Bakunci Taron Ministocin Cikin Gida Na Kungiyar ECO October 25, 2025 Jakadan Iran A Majalisar Dinkin Duniya Ya Yi Kiran Da A Nisanci Siyasantar Da Kwamitin Tsaron Majalisar October 25, 2025 Tsohon Shugaban Hukumar Leken Asirin Dakarun IRGC Ya Ce: Yakin Kwanaki 12 Kan Iran Ya Canza Tunanin Makiya October 25, 2025 Rear Admiral Sayyari: Sojojin Iran A Shirye Suke Su Fuskanci Kowace Barazana October 25, 2025 Shugaban Kasar Venezuela Ya Ce; Amurka Tana Son Kaddamar Da Yaki Kan Kasarsa October 25, 2025 Bangarorin Falasdinawa Sun Amince Da Shirin Gudanar Da Zirin Gaza Nan Gaba October 25, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma
  • Hamas : Netanyahu Yana kokarin wargaza yarjejeniyar tsagaita wuta
  • Sojojin Isra’ila Sun Kai Hare-Hare Kan Yankin Gaza A Matsayin Karya Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta
  • Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu
  • Hamas Ta Ce: Kungiyar Ta Ba Da ‘Yanci Ga Masu Shiga Tsakani Zabar Membobin Kwamitin Gudanar Da Gaza
  • Hamas ta sake jaddada wajabcin aiwatar da Shirin tsagaita wuta a Gaza
  • Ba zan sake tsayawa takara ba, zan bai wa matasa dama — Dasuki
  • Hamas : Ba za mu bari Isra’ila ta sami wata hujja ta ci gaba da yaki a Gaza ba
  • Iran Ta Ki Zuwa Taron Sherme-Sheikh Ne Saboda Kar Ta Zama  Mai Shaidar Zur Akan Kisan Kiyashin Gaza