Ɗalibi ya kashe abokinsa, ya binne shi a rami a Filato
Published: 27th, October 2025 GMT
Wani ɗalibin Jami’ar Jos da ke Jihar Filato, ya kashe abokinsa, wanda shi ma ɗalibi ne a jami’ar, sannan ya binne gawarsa a bayan gidansu.
Wanda aka kashe mai suna Peter Mafuyai, ɗalibi ne da ke shekara ta uku a sashen hada-hadar kuɗaɗen banki.
Dangote na shirin faɗaɗa matatarsa don zama mafi girma a duniya Ba zan sake tsayawa takara ba, zan bai wa matasa dama — DasukiAna zargin Nanpon Timnan da ke ajin shekara ta biyu daga sashen karatun harkar noma, da kashe shi sannan ya binne shi a rami.
Rahotanni sun bayyana cewar ɗaliban abokan juna ne sosai.
An ruwaito sun fita ƙwallon ƙafa, daga nan suka wuce wani waje sannan suka dawo gida.
“Da suka dawo Nanpon ya ɗauko adda. Abokansa da suke zaune tare a cikin gidan suka tambaye shi me zai yi da addar, sai ya ce yana son amfani da ita ne,” in ji wata majiya.
“Bayan haka sai ya sari abokinsa Peter da addar. Sauran abokan suka fara ihu suna tambayar dalilin da ya sa ya yi hakan, amma bai ba su amsa ba. Suka fita neman taimako, amma kafin su dawo, tuni ya binne gawar a bayan gidan.”
’Yan sanda sun riga sun gayyaci sauran abokan don yi musu tambayoyi, kuma ana ci gaba da bincike.
Zuwa yanzu dai babu cikakken bayani kan dalilin da ya sa ya yi kisan, sai dai wata majiya ta ce wataƙila sun sama saɓani.
Sakamakon yajin aikin ASUU da ake yi a jami’ar, babu ɗalibai ya bare a samu cikakken bayani ba.
Da aka tuntuɓi Shugabar riƙon ƙwarya ta Sashen Watsa Labarai na jami’ar, Tongdyen Dachung, ta ce ba za ta iya yin magana kan lamarin ba tukunna, domin tana buƙatar tabbatar da wasu bayanai.
Ita kuwa Shugabar Ƙungiyar Ɗaliban Jami’ar (SUG), Jane Pwajok, ta ce lamarin yana hannun ’yan sanda.
Ƙoƙarin jin ta bakin kakakin ’yan sandan Jihar Filato, Alfred Alabo, bai yi nasara ba, domin ba ya ɗaga waya.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Matsalar kashe-kashe a Nijeriya ba ta da alaƙa da addini — Femi Kayode
Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama, Cif Femi Fani-Kayode, ya bayyana cewa matsalar kashe-kashen da ake fama da su a sassa daban-daban na ƙasar nan ba ta da alaƙa da addini, illa dai ayyukan miyagu da ke kashe Musulmi da Kirista ba tare da la’akari da bambancin addini ba.
Fani-Kayode ya bayyana hakan ne a yayin da yake jawabi a matsayin bako mai jawabi a taron cika shekaru 35 da kafuwar Cocin Anglican da ke garin Kafanchan a Jihar Kaduna.
NSCDC ta yi alhinin mutuwar Kwamishinan Tsaron Gombe An kama mutum 25 kan zargin shirya auren jinsi a KanoTsohon Ministan ya ce lokaci ya yi da ‘yan Najeriya za su dawo daga rakiyar mutanen da ke amfani da addini wajen raba kan al’umma, yana mai cewa masu kashe Kiristoci su ne dai ke kashe Musulmi.
Ya buƙaci mabiya addinan biyu da su rungumi zaman lafiya, haɗin kai da fahimtar juna, tare da guje wa duk wani yunƙurin na kawo rarrabuwa ko tashin hankali.
A nasa ɓangaren, Babban Mai Shari’a na Jihar Kaduna, Barista James Kanyip, wanda ya wakilci Gwamnan Jihar, Sanata Uba Sani, ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar na ci gaba da kare ‘yancin addini da tabbatar da haɗin kai da shugabannin addinai, musamman masu wa’azin zaman lafiya da jituwa.
Shi ma Bishop Markus Dogo na Cocin Anglican da ke Kafanchan, ya bayyana irin ayyukan jin ƙai da cocin ya gudanar cikin shekaru 35, ciki har da gina makarantu, asibitoci da cibiyoyin koyon sana’o’i don tallafa wa marasa galihu.
Haka kuma, Sanatan Kaduna ta Kudu, Barista Sunday Marshall Katung, wanda ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Jema’a da Sanga, Hon. Daniel Amos ya wakilta, ya yaba wa Gwamna Uba Sani bisa yadda yake tafiyar da mulki cikin adalci da rashin nuna wariya ga kowane ɓangare na jihar.
Taron ya samu halarci manyan shugabannin addini, na siyasa da na al’umma, inda suka jaddada muhimmancin zaman lafiya da haɗin kai a matsayin ginshiƙai na ci gaban Najeriya.