Ɗalibi ya kashe abokinsa, ya binne shi a rami a Filato
Published: 27th, October 2025 GMT
Wani ɗalibin Jami’ar Jos da ke Jihar Filato, ya kashe abokinsa, wanda shi ma ɗalibi ne a jami’ar, sannan ya binne gawarsa a bayan gidansu.
Wanda aka kashe mai suna Peter Mafuyai, ɗalibi ne da ke shekara ta uku a sashen hada-hadar kuɗaɗen banki.
Dangote na shirin faɗaɗa matatarsa don zama mafi girma a duniya Ba zan sake tsayawa takara ba, zan bai wa matasa dama — DasukiAna zargin Nanpon Timnan da ke ajin shekara ta biyu daga sashen karatun harkar noma, da kashe shi sannan ya binne shi a rami.
Rahotanni sun bayyana cewar ɗaliban abokan juna ne sosai.
An ruwaito sun fita ƙwallon ƙafa, daga nan suka wuce wani waje sannan suka dawo gida.
“Da suka dawo Nanpon ya ɗauko adda. Abokansa da suke zaune tare a cikin gidan suka tambaye shi me zai yi da addar, sai ya ce yana son amfani da ita ne,” in ji wata majiya.
“Bayan haka sai ya sari abokinsa Peter da addar. Sauran abokan suka fara ihu suna tambayar dalilin da ya sa ya yi hakan, amma bai ba su amsa ba. Suka fita neman taimako, amma kafin su dawo, tuni ya binne gawar a bayan gidan.”
’Yan sanda sun riga sun gayyaci sauran abokan don yi musu tambayoyi, kuma ana ci gaba da bincike.
Zuwa yanzu dai babu cikakken bayani kan dalilin da ya sa ya yi kisan, sai dai wata majiya ta ce wataƙila sun sama saɓani.
Sakamakon yajin aikin ASUU da ake yi a jami’ar, babu ɗalibai ya bare a samu cikakken bayani ba.
Da aka tuntuɓi Shugabar riƙon ƙwarya ta Sashen Watsa Labarai na jami’ar, Tongdyen Dachung, ta ce ba za ta iya yin magana kan lamarin ba tukunna, domin tana buƙatar tabbatar da wasu bayanai.
Ita kuwa Shugabar Ƙungiyar Ɗaliban Jami’ar (SUG), Jane Pwajok, ta ce lamarin yana hannun ’yan sanda.
Ƙoƙarin jin ta bakin kakakin ’yan sandan Jihar Filato, Alfred Alabo, bai yi nasara ba, domin ba ya ɗaga waya.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Sakkwatawa na murnar kisan da sojoji suka yi wa mataimakin Bello Turji
Al’ummar ƙaramar hukumar Sabon Birni da ke jihar Sakkwato sun bayyana farin ciki bayan samun labarin kashe fitaccen ɗan bindiga da ya dade yana addabar yankin gabashin jihar, Kacalla Kallamu.
Rundunar Sojoji ta 8 ta hallaka jagoran ’yan bindiga, Kachalla Kallamu, a wani samamen haɗin gwiwa da aka kaddamar a ƙaramar hukumar Sabon Birni.
Dalibin jami’a ya rasu a hatsarin motar murnar kammala jarabawa Iya sojojin da ke tsaron Seyi Tinubu sun isa su samar da tsaro a Benin – SoyinkaWata majiyar soja da ta tabbatar da lamarin ga manema labarai a ranar Talata ta bayyana samamen a matsayin “babbar asara ga cibiyar ’yan bindigar Bello Turji,” tana mai cewa Kallamu shi ne babban na hannun daman Turji.
A cewar majiyar, an kashe Kallamu tare da wani daga cikin manyan masu samar wa Turji kayayyakin aiki a lokacin samamen da aka gudanar da safe a kauyen Kurawa ranar Litinin.
Majiyar ta ƙara da cewa aikin ya samu muhimmiyar gudunmuwar kungiyoyin sa‑kai na yankin.
“Mun dade muna bibiyar Kallamu. Kashe shi wata babbar nasara ce wajen raunana karfin ’yan bindigar da ke Sabon Birni da kewaye,” in ji majiyar.
Mamacin, wanda asalin ɗan Garin Idi ne a Sabon Birni, ya dade yana addabar al’ummar yankin.
Ana zargin ya gudu zuwa Jihar Kogi bayan ya tsere wa luguden wutar sojoji a watan Yuni 2025, amma ya sake shigowa yankin kwanan nan ba tare da an sani ba.
Majiyar ta yaba da ƙarin bayanan sirri da ake samu daga al’ummomin yankin, tana mai cewa haɗin kai tsakanin mazauna yankin da jami’an tsaro ya taka muhimmiyar rawa wajen nasarorin baya‑bayan nan.
Manema labarai sun ruwaito cewa an ci gaba da murnar labarin a Sabon Birni, yayin da mashawarcin musamman ga Gwamna Ahmad Aliyu kan harkokin tsaro, Kanal Ahmed Usman (mai ritaya), ya yaba wa dakarun bisa “ci gaba da jajircewa da ƙwarewa” wajen yaƙi da ’yan bindiga.
Mutanen garin Sabon Birni sun fito maza da mata suna murnar nasarar da aka samu, har suna cewa suna jin wannan rana kamar ta Sallah.
Sun yi fatan a ci gaba da samun nasarori irin wannan domin kawar da ’yan bindiga a yankin, a jihar, da kuma Arewacin Najeriya gaba ɗaya.