Aminiya:
2025-10-26@16:51:06 GMT

Majalisa ta amince a ƙirƙiro sabbin jihohi 6 a Najeriya

Published: 26th, October 2025 GMT

Kwamitin Haɗin Gwiwa na Majalisar Dattawa da Majalisar Wakilai kan gyaran kundin tsarin mulkin Najeriya, ya amince da buƙatar ƙirƙiro sabbin jihohi guda shida.

Wannan mataki na cikin abin da aka cimma a ƙarshen taron kwana biyu da aka gudanar a Legas, ƙarƙashin jagorancin Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I.

Jibrin, da Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai, Benjamin Kalu.

Matsalar kashe-kashe a Nijeriya ba ta da alaƙa da addini — Femi Kayode Boko Haram na amfani da jirage marasa matuƙa wajen kai hare-hare — Zulum

A cewar kwamitin, an tattauna kan buƙatu 69, ciki har da buƙatun ƙirƙirar jihohi 55 da kuma ƙananan hukumomi 278.

Daga cikin buƙatun ƙirƙirar jihohi 55 da aka gabatar, kwamitin ya amince da ƙirƙirar jihohi shida; ɗaya daga kowanne yanki.

“Za mu binciki dukkanin buƙatun ƙirƙirar jihohi 55 da aka gabatar domin gano inda za a fitar da sababbin jihohi shida.

“Za mu yi wa kowa adalc,” in ji ɗaya daga cikin mambobin kwamitin daga yankin Arewa Maso Yamma.

Idan Majalisar Tarayya ta amince da wannan yunƙuri gaba ɗaya, Najeriya za ta koma tana da jihohi 42 maimakon 36 da ake da su yanzu.

Wannan mataki, a cewar wani babban jami’in majalisar, “Yana nuna adalci da daidaito ga dukkanin yankuna,” kuma za a gabatar da rahoton kwamitin ga duka majalisun a farkon makon Nuwamba.

Sanata Barau, ya ce burin majalisar shi ne tabbatar da cewa duk wasu sauye-sauye da za a yi wa kundin tsarin mulki su kasance waɗanda za su amfani al’umma, tare da cika alƙawarin da aka ɗauka na tura sabon ƙudiri zuwa majalisun dokoki na jihohi kafin ƙarshen wannan shekara.

“Mun shafe sama da shekaru biyu muna taro da al’umma, ƙungiyoyi, da masana domin samun ra’ayoyi game da yadda za a inganta tsarin mulkin ƙasar nan,” in ji shi.

Taron na Legas ya kasance dama ga mambobin majalisar domin su nazarci sauye-sauyen da ake son yi, musamman batutuwan da suka shafi ƙirƙirar sabbin jihohi, daidaita iyakoki, da ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gyaran Kundin Tsarin Mulki iyakoki Kwamiti Majalisar Dattawa Majalisar Wakilai Sanata Barau ƙirƙirar jihohi

এছাড়াও পড়ুন:

Dan Majalisar Dokokin Tarayyar Turai Ya Ce: Dole Ne A Hakunta Isra’ila Kan Laifukan Da Ta Aikata

Memba a Majalisar Tarayyar Turai ya bayyana cewa: Zaman lafiya na gaske yana buƙatar ɗaukar matakin hukunta Isra’ila

Dan Majalisar Dokokin Turai ta Ireland (MEP) Barry Andrews ya jaddada cewa: Daukan matakin hukunta haramtacciyar kasar Isra’ila kan munanan laifukan da ta aikata a Zirin Gaza ita ce hanya daya tilo da za a cimma zaman lafiya na gaskiya da dorewa, yana mai kira ga Tarayyar Turai da ta ci gaba da zabar sanya takunkumi kan Isra’ila.

Jawabin Andrews ya zo ne a wata hira da kamfanin dillancin labarai na Anadolu na kasar Turkiyya, wanda ya yi daidai da taron Tarayyar Turai da aka gudanar a Brussels ranar Alhamis da ta gabata, wanda ya tattauna makomar dangantakar Tarayyar Turai da Isra’ila bayan tsagaita wuta na baya-bayan nan a Gaza.

Andrews ya ce, “Kwarewar ƙasarsa a cikin tsarin zaman lafiya na Ireland ya nuna cewa; Ba za a iya cimma zaman lafiya ba tare da adalci da rikon amana ba. Sulhu tsakanin Isra’ila da Falasdinawa yana buƙatar goyon bayan ƙasashen duniya mai ɗorewa, amma ba zai yi nasara ba idan duniya ta yi watsi da laifukan da aka aikata.”

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Mayakan Kungiyar Kurdawa Ta PKK Sun Fice Daga Turkiyya Zuwa Iraki October 26, 2025  Iran Za Ta Karbi Bakuncin  Taron Kungiyar Tattalin Arziki TA “Eco” A Gobe Litinin October 26, 2025  Bahrain: Fursunoni 90 Suna Yajin Cin Abinci Saboda Neman ‘Yanci October 26, 2025 Shugaban Kasar Nigeria Ya Yi Sauye-sauye A Rundunonin Sojan Kasar October 26, 2025 Iran Ta Ki Zuwa Taron Sherme-Sheikh Ne Saboda Kar Ta Zama  Mai Shaidar Zur Akan Kisan Kiyashin Gaza October 26, 2025 Jami’ar ABU Ta Karyata Zargin Da Ake yi Na Kera Makamin Nukiliya A Asirce October 25, 2025 M D D Ta ce Akalla Mutane miliyan 1.5 Ne Ke Bukatar Taimakon Gaggawa A Gaza October 25, 2025 Tony Balai Na Fuskantar Turjiyar Kasashen Larabawa Game Da Rawar Da Zai Taka A Gaza. October 25, 2025 Yau Ne Ake Gudanar Da Zaben Shugaban Kasa  A Ivory Coast October 25, 2025 Iran Za ta Karbi Bakunci Taron Ministocin Cikin Gida Na Kungiyar ECO October 25, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ya Ce: Iran, Rasha Da China Sun Aike Da Sako Mai Muhimmanci
  • Dan Majalisar Dokokin Tarayyar Turai Ya Ce: Dole Ne A Hakunta Isra’ila Kan Laifukan Da Ta Aikata
  • Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu
  • Farfesa Muhammed Khalid Othman Ya Zama Sabon Shugaban Jami’ar Tarayya Ta Dutsinma
  • Jakadan Iran A Majalisar Dinkin Duniya Ya Yi Kiran Da A Nisanci Siyasantar Da Kwamitin Tsaron Majalisar
  • Muna Duba Ƙudirin Ƙirƙiro Jihohi 55 – Barau Jibrin
  • Gwamnatin Jihar Sokoto Ta Amince da Sauya Amfani da Naira Biliyan 526 a Kasafin Kuɗin 2025
  • Majalisar Tattalin Arziki Ta Amince da Shirin Gyara Cibiyoyin Horar da Jami’an Tsaro
  • NAJERIYA A YAU: Me Dawowar Hare-hare Kan Sojoji Ke Nufi A Arewa Maso Gabas?