Matsalar kashe-kashe a Nijeriya ba ta da alaƙa da addini — Femi Kayode
Published: 26th, October 2025 GMT
Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama, Cif Femi Fani-Kayode, ya bayyana cewa matsalar kashe-kashen da ake fama da su a sassa daban-daban na ƙasar nan ba ta da alaƙa da addini, illa dai ayyukan miyagu da ke kashe Musulmi da Kirista ba tare da la’akari da bambancin addini ba.
Fani-Kayode ya bayyana hakan ne a yayin da yake jawabi a matsayin bako mai jawabi a taron cika shekaru 35 da kafuwar Cocin Anglican da ke garin Kafanchan a Jihar Kaduna.
Tsohon Ministan ya ce lokaci ya yi da ‘yan Najeriya za su dawo daga rakiyar mutanen da ke amfani da addini wajen raba kan al’umma, yana mai cewa masu kashe Kiristoci su ne dai ke kashe Musulmi.
Ya buƙaci mabiya addinan biyu da su rungumi zaman lafiya, haɗin kai da fahimtar juna, tare da guje wa duk wani yunƙurin na kawo rarrabuwa ko tashin hankali.
A nasa ɓangaren, Babban Mai Shari’a na Jihar Kaduna, Barista James Kanyip, wanda ya wakilci Gwamnan Jihar, Sanata Uba Sani, ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar na ci gaba da kare ‘yancin addini da tabbatar da haɗin kai da shugabannin addinai, musamman masu wa’azin zaman lafiya da jituwa.
Shi ma Bishop Markus Dogo na Cocin Anglican da ke Kafanchan, ya bayyana irin ayyukan jin ƙai da cocin ya gudanar cikin shekaru 35, ciki har da gina makarantu, asibitoci da cibiyoyin koyon sana’o’i don tallafa wa marasa galihu.
Haka kuma, Sanatan Kaduna ta Kudu, Barista Sunday Marshall Katung, wanda ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Jema’a da Sanga, Hon. Daniel Amos ya wakilta, ya yaba wa Gwamna Uba Sani bisa yadda yake tafiyar da mulki cikin adalci da rashin nuna wariya ga kowane ɓangare na jihar.
Taron ya samu halarci manyan shugabannin addini, na siyasa da na al’umma, inda suka jaddada muhimmancin zaman lafiya da haɗin kai a matsayin ginshiƙai na ci gaban Najeriya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Femi Fani Kayode
এছাড়াও পড়ুন:
Gwarzon Ma’aikacin Lafiya Na Shekarar 2025 Dakta Seidu Adebayo Bello
Aƙidar Dr Bello abu ne mai saƙin gaske kuma akwai hikima a ciki sosai. Shi ne kuma samar da ingantacciyar kiwon lafiya wand aba wai sai kana da kuɗi mai yawa ba.
Tsarinsa shi ne haɗa yi wa mutane aiki, ilimantar da su tared fda kuma tsugunar da su. Wannan mataki ne da yake tabbatar da an samun cikin gaggawa da kuma sauƙin gaske..
Daga Legas zuwa Kano, daga Ondo zuwa Kuros Riba, kungiyar CFDF tana tafiya da kayan aiki na tafi da gidanka da kuma rundunar likitoci masu tiyata na sa kai, masu aikin jinya, da ma’aikatan jinya. Kowace manufa asibiti ce mai motsi – duba marasa lafiya, yin hadaddun tiyata, da bayar da shawarwari da tallafin abinci mai gina jiki ga iyalai waɗanda a da suna tunanin warkarwa ba ta isa ba.
A ƙarƙashin shugabancinsa, gidauniyar ta zama wani samfur na yadda za a gudanar da samar wa da al’umma kiwon lafiya mai sauƙi kuma mai inganci, musamman tiyata a fuska.
Canza Tsari Ba Canza Fuska kawai Ba
Cutar Cleft lips da palates sun daɗe suna takura wa al’umma. Yara na kunyar fita cikin mutane, ana kuma tsangwamar iyaye mata da iyalai inda ake ɗora musu lafin aukuwar cutar.
Ayyukan Dr Bello suna kula da waɗannan yanayi n acuta, ana kuma amfani da tiyatar da ake yi wajen yaƙar jahilci. Duk gangamin da aka ana amfani da shi wajen faɗakar da al’umma akan ainihin yadda cutar take tare da kuma ƙarfafa wa al’umma kawo mara lafira domin amagani a kan lokaci.
Ta hanyar ilimantar da al’umma da kuma bibiyar mara lafiya bayan an yi masa tiyata a yanzu an samu rage tsoro da jin kunya a zukatan mutane, mutane kuma na ƙara fahimtar cewa, wannna cut aba tsinuwa ba ne abu ne da za a iya warkar da shi ta hanyar kimiyya da fasaha.
Likitan Tiyata, Masani kuma bawan Allah
Cikakken masani kuma ƙwararren likitan tiyata a a babban asibitin fadar shugaban ƙasa, Dr Bello yana shugabanci cikin matsuwa da hangen nesa.
Mamba ne na ƙungiyoyi da dama da suka haɗa da ‘National Postgraduate Medical College of Nigeria (FMCDS), West African College of Surgeons (FWACS), International Congress of Oral Implantologists (FICOI) da kuma Global Congress of Implantology (FGCOI).
A mastayoinsa na malamai, Dr Bello ya karantar tare da sa ido a ayyukan matasan likitoci masu tasowa da dama, ta haka za a tabbatar da sun gaji irin ƙwarewarsa tare da samar wa al’umma fata na gari.
Ya kuma rubuta muƙaloli na kimiyya fiye da 35 ya kuma ƙirƙiro ‘International Craniofacial Academy (ICA) a Abuja, ya kuma ci gaba da yi wa mutane tiyata kyauta ba tare da ko sisi ba.
Abin Ya Fi Batun Ɗakin Tiyata
A wajen asibitin, Dr Bello yana da alaƙa da tushen sa. Yana riƙe da matsayin Aare musulmi na Ago Are, shugaban kungiyar ci gaban Oke Ogun (reshen Abuja), kuma ya shahara dawajen yi wa al’umma hidima.
Amma ga marasa lafiyarsa, “likita ne kawai mai sanya murmushi ga fuskan al’umma.”
Samar da Kiwon Lafiya Mai Dorewa
A shekarar 2010 aka kafa gidauniyar “ Cleft and Facial Deformity Foundation” an kuma gudanar da tiyata sama da 50 a duk yankuna shida na ƙasar nan.
Misalin haɗin gwiwarsa tare da gwamnatocin jihohi, asibitocin koyarwa, da al’ummomin gida ya tabbatar da cewa ingantaccen tsarin kiwon lafiya yana buƙatar ingantattun ababen more rayuwa.
Alƙalumma Basa Ƙarya
An yi tiyata 2,600 kyauta, An kammala ayyukan jinya 50 a faɗin Nijeriya
Ɗaruruwan ma’aikatan lafiya sun sami horo a yankunan karkara
Dubban iyalai ne aka faɗakar a kan rashin fahimtasu ga yadda cutar take.
Rayuwar Da Ke Taimakawa Motsi
Dr Bello ya zaburar da masu aikin sa kai a Yammacin Afirka don yin hidima ga marasa lafiyata hanyar daidaita tsakanin manufofi da aiki, ya nuna cewa ƙudurin likitan fiɗa ɗaya zai iya zama matakin samun nasara ga kiwon lafiyar al’umma.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA