Aminiya:
2025-10-30@14:40:18 GMT

Majalisa ta amince Tinubu ya karɓo rancen dala biliyan 2.35

Published: 30th, October 2025 GMT

Majalisar Tarayya, ta amince da buƙatar Shugaba Bola Ahmed Tinubu na karɓo rancen dala biliyan 2.35 domin cike giɓin kasafin kuɗin shekarar 2025.

Dukkanin Mjalisun sun amince da buƙatar ne a ranar Laraba, bayan sun duba rahoton kwamitin karɓar basussuka na cikin gida da na waje.

Zargin Kisan Kiristoci: ’Yan majalisar Amurka sun yi amfani da bayanai marasa tushe — Gwamnati ACF ta mara wa gwamnatin Tinubu baya

Haka kuma, majalisar ta amince da buƙatar Tinubu na fitar da dala miliyan 500 domin samar da muhimman ayyuka kamar faɗaɗa hanyoyin samun kuɗi ga ƙasar nan.

A cikin wasiƙar da ya aike wa majalisar tun a farkon watan nan, Shugaba Tinubu, ya bayyana cewa neman rancen ya zama dole domin aiwatar da kasafin kuɗin 2025.

Kasafin wanda ya ƙunshi Naira tiriliyan 9.28 na nufin cike giɓin da ake da shi a kasafin 2025.

Ya ce hakan zai taimaka wajen kauce wa kasa biyan bashi da kuma bin inganta ƙa’idojin kasuwar hada-hadar bashi ta duniya.

“Jimillar kuɗin da za a nema daga waje; dala biliyan 1.229 na sabon rance da dala biliyan 1.118 na sake biyan tsohon bashi zai kai dala biliyan 2.347,” in ji wasiƙar.

’Yan majalisa sun bayyana cewa rancen zai taimaka wa gwamnati ci gaba da aiwatar da muhimman ayyukan raya ƙasa da kuma daidaita tattalin arziƙi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: rance dala biliyan

এছাড়াও পড়ুন:

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

Sai dai gwamnatin Tinubu ta mayar da martani, tana cewa jam’iyyar ADC kawai tana adawa ne da nasarorin da gwamnati ke samu.

Hadimin shugaban kasa, Abdulaziz Abdulaziz, ya ce: “Da farko ‘yan adawa suna ƙorafi cewa abinci ya yi tsada. Yanzu da gwamnati ta ɗauki matakai don rage tsada, sai kuma suke kuka.”

A watan Satumba 2025, Shugaba Tinubu ya umarci kwamiti na musamman na gwamnati da ya ɗauki matakan gaggawa don rage tsadar abinci a faɗin ƙasar nan.

Duk da haka, wasu manoma na kukan cewa matakan sun jawo musu asara saboda tsadar kayan noman da suke amfani da su.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai ‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa October 29, 2025 Manyan Labarai Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II October 29, 2025 Manyan Labarai Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260 October 28, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnan Bauchi na neman ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi 29
  • Tinubu Ya Amince Da Ƙara Harajin Shigo Da Man Fetur Da Dizal Zuwa Kashi 15
  • Atiku Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Sauya Sunayen Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa
  • Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU
  • Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya
  • Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC
  • Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC
  • Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Abinci Ba – ADC
  • ‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa