Alassane Ouattara ya lashe zaɓen Ivory Coast karo na huɗu
Published: 27th, October 2025 GMT
Shugaba Alassane Ouattara, ya sake lashe zaɓen shugabancin ƙasar Ivory Coast wanda ya ba shi sabon wa’adin mulki a karo na huɗu.
Ouattara mai shekaru 83, ya samu kashi 89.77 cikin 100 na ƙuri’un da aka kaɗa, kamar yadda hukumar zaɓe ta ƙasa ta tabbatar a ranar Litinin.
Tinubu ya gana da sabbin hafsoshin tsaro An kashe wasu makiyaya 10 a KebbiFiye da mutane miliyan tara ne suka cancanci kada ƙuri’a a zaben da aka gudanar a ranar Asabar, wanda aka gudanar cikin yanayi na fargaba, bayan da manyan abokan hamayyarsa biyu — tsohon shugaban ƙasa Laurent Gbagbo da tsohon shugaban Credit Suisse, Tidjane Thiam — aka hana su tsayawa takara.
Sakamakon ya nuna cewa, duk da ƙarancin fitowar masu jefa ƙuri’a a wasu sassan ƙasar, Ouattara ya samu rinjaye har ma a yankunan da ake ganin masu adawa ke da tasiri.
Tsohon Ministan Kasuwanci, Jean-Louis Billon ne ya zo na biyu da kashi 3.09 cikin 100, sai kuma matar tsohon shugaban ƙasa, Simone Gbagbo ta samu kaso 2.42, yayin da hukumar zaɓe ta bayyana cewa adadin waɗanda suka kaɗa ƙuri’a sun kai kashi 50.10 cikin 100 — kwatankwacin na shekarar 2020.
Masana harkokin siyasa sun ce rashin halartar manyan ‘yan adawa da kiran su na a ƙaurace wa zaɓen ya sa jama’a da dama suka ƙi ita kaɗa ƙuri’a.
Sai dai duk da nasarar da Ouattara ya samu, jam’iyyun adawa sun ƙi amincewa da sakamakon, inda suka buƙaci a gudanar da sabon zaɓe.
Rahotanni sun ce aƙalla mutane takwas ne suka mutu yayin tarzomar da ta barke kafin zaben, lamarin da ya sa gwamnati ta kafa takunkumin fita da dare a wasu yankuna tare da jibge jami’an tsaro 44,000 don tabbatar da tsaro.
A yanzu haka dai harkokin yau da kullum kamar yadda aka saba sun kankama a birnin Abidjan bayan sanar da sakamakon zaɓen da wasu jaridu ke yabawa a matsayin “zaɓe na kwanciyar hankali,” yayin da wasu ke cewa ya sake nuna rarrabuwar kawuna a ƙasar.
Ouattara ya fara hawa mulkin Ivory Coast ne bayan rikicin zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2010-2011 tsakaninsa da Laurent Gbagbo, wanda ya yi sanadin mutuwar fiye da mutane 3,000 daga ɓangarorin magoya bayansu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Alassane Ouattara Ivory Coast Ouattara ya
এছাড়াও পড়ুন:
Sakkwatawa na murnar kisan da sojoji suka yi wa mataimakin Bello Turji
Al’ummar ƙaramar hukumar Sabon Birni da ke jihar Sakkwato sun bayyana farin ciki bayan samun labarin kashe fitaccen ɗan bindiga da ya dade yana addabar yankin gabashin jihar, Kacalla Kallamu.
Rundunar Sojoji ta 8 ta hallaka jagoran ’yan bindiga, Kachalla Kallamu, a wani samamen haɗin gwiwa da aka kaddamar a ƙaramar hukumar Sabon Birni.
Dalibin jami’a ya rasu a hatsarin motar murnar kammala jarabawa Iya sojojin da ke tsaron Seyi Tinubu sun isa su samar da tsaro a Benin – SoyinkaWata majiyar soja da ta tabbatar da lamarin ga manema labarai a ranar Talata ta bayyana samamen a matsayin “babbar asara ga cibiyar ’yan bindigar Bello Turji,” tana mai cewa Kallamu shi ne babban na hannun daman Turji.
A cewar majiyar, an kashe Kallamu tare da wani daga cikin manyan masu samar wa Turji kayayyakin aiki a lokacin samamen da aka gudanar da safe a kauyen Kurawa ranar Litinin.
Majiyar ta ƙara da cewa aikin ya samu muhimmiyar gudunmuwar kungiyoyin sa‑kai na yankin.
“Mun dade muna bibiyar Kallamu. Kashe shi wata babbar nasara ce wajen raunana karfin ’yan bindigar da ke Sabon Birni da kewaye,” in ji majiyar.
Mamacin, wanda asalin ɗan Garin Idi ne a Sabon Birni, ya dade yana addabar al’ummar yankin.
Ana zargin ya gudu zuwa Jihar Kogi bayan ya tsere wa luguden wutar sojoji a watan Yuni 2025, amma ya sake shigowa yankin kwanan nan ba tare da an sani ba.
Majiyar ta yaba da ƙarin bayanan sirri da ake samu daga al’ummomin yankin, tana mai cewa haɗin kai tsakanin mazauna yankin da jami’an tsaro ya taka muhimmiyar rawa wajen nasarorin baya‑bayan nan.
Manema labarai sun ruwaito cewa an ci gaba da murnar labarin a Sabon Birni, yayin da mashawarcin musamman ga Gwamna Ahmad Aliyu kan harkokin tsaro, Kanal Ahmed Usman (mai ritaya), ya yaba wa dakarun bisa “ci gaba da jajircewa da ƙwarewa” wajen yaƙi da ’yan bindiga.
Mutanen garin Sabon Birni sun fito maza da mata suna murnar nasarar da aka samu, har suna cewa suna jin wannan rana kamar ta Sallah.
Sun yi fatan a ci gaba da samun nasarori irin wannan domin kawar da ’yan bindiga a yankin, a jihar, da kuma Arewacin Najeriya gaba ɗaya.