An kai ƙarar malamai 2 kan zargin ɓatanci ga Annabi a Kaduna
Published: 29th, October 2025 GMT
Wata gamayyar malaman addinin Musulmai ƙarƙashin inuwar Concerned Ulama of Sunnah ta aika da ƙorafi zuwa ga Gwamnatin Jihar Kaduna tana zargin wasu malamai biyu da yin ɓatanci ga Annabi Muhammad (S.A.W).
Ana zargin malaman ne da yi batancin a cikin wa’azozinsu na kafafen sada zumunta.
Gwamnatin Kamaru za ta gurfanar da Issa Tchiroma a kotu kan zargin tayar da zaune tsaye Uwa da ’yarta sun nitse a hatsarin jirgin ruwa a BornoƘorafin, wanda malamai goma sha shida (16) suka sanya wa hannu, ƙarƙashin jagorancin Shaikh Umar Shehu Zaria da Malam Muhammad Sani Abubakar, Babban Limamin Masallacin Juma’a na Hayin Na’iya, ya bukaci gwamnatin jihar da ta gaggauta ɗaukar mataki.
A cewar masu ƙorafin, ayyukan waɗannan malamai biyu “na iya janyo tashin hankali a ƙasarmu mai albarka idan aka bar su haka.”
Sun roƙi hukumomi da su gayyace su domin tattaunawa idan ya zama dole, ko kuma su dakatar da su, suna gargaɗin cewa rashin ɗaukar mataki “na iya haifar da tashin hankali da rikici wanda gwamnati ba za ta so hakan ba.”
Kungiyar ta bayyana cewa batun ya wuce na son rai, yana da alaƙa kai tsaye da muhimman ƙa’idodin addinin Musulunci.
“Akwai imani na asali cikin al’ummar Musulmi na girmamawa da kare mutuncin Annabi Muhammad (S.A.W). Shi ne asalin alheri ga kowanne Musulmi a duniya da lahira,” in ji ƙorafin”
Masu ƙorafin sun ambaci shari’ar Musulunci da maganganun manyan malamai dake nuna tsananin laifin batanci ga Annabi.
Sun kuma roƙi gwamnatin jihar da ta gaggauta ɗaukar mataki don hana rikici.
“Jihar Kaduna ta sha fama da rikice-rikicen ƙabilanci da na addini a baya, amma da taimakon Allah da jajircewar gwamnati, an shawo kan da dama daga cikin lamarin,” in ji su.
A martanin da ya bayar, Daraktan Hukumar Huldar Addinai ta Jihar Kaduna, Tahir Umar Tahir, ya tabbatar da karɓar ƙorafin kuma ya tabbatar wa malamai cewa gwamnati za ta duba shi.
“Mun karɓi ƙorafinsu a madadin Gwamnan Jihar, Sanata Uba Sani, kuma da yardar Allah za mu duba wannan batu. Za a ɗauki matakan da suka dace don hana tashin hankali,” in ji Kwamishinan.
Ya ƙara da cewa gwamnati za ta ci gaba da tsayawa wajen tabbatar da zaman lafiya da haɗin kai tsakanin addinai:
Tahir ya kuma roƙi shugabannin da malaman addinai da su yi hattara a cikin wa’azozinsu, yana gargaɗin su guji duk wani saƙo da zai iya haddasa rarrabuwar kai ko tashin hankali a cikin jihar.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda APC Da ADC Ke Amfana Da Rikicin Jam’iyyar PDP
PDP wanda ke da gwamnonin 11 bayan zaben 2023, yanzu tana da biyar kawai tare da karin wasu suna nuna suna son barin jam’iyyar.
Yawancin gwamnonin da suka sauya sheka a cikin wannan lokaci sun koma APC, yayin da jam’iyyar Accord ta samu guda daya.
Gwamnonin da suka bar PDP zuwa APC su ne Umoh Eno na Akwa Ibom da Sheriff Oborebwori na Delta da Douye Diri na Bayelsa da Peter Mbah na Jihar inugu. Gwamnan Jihar Taraba, Agbu Kefas, ya dade yana son barin PDP kuma yanzu yana jiran lokaci mai ya yi ne ya shiga APC.
Akwai fargaba cewa gwamnonin Caleb Muftwang na Jihar Filato da gwamnan Zamfara, Dauda Lawal ma na iya canza sheka. Gwamnonin PDP kadai da suka bayyana a fili cewa za su tsaya cikin jam’iyyar don gyara al’amuran gida su ne gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammad da abokin aikinsa na Jihar Oyo, Seyi Makinde, yayin da Ahmadu Umaru Fintiri na Adamawa ya bayyana tamkar yana son sauya sheka.
Rikicin PDP y afara kuno kai ne tun bayan zabukan 2023, baya ga gwamnoni, jam’iyyar ta rasa karin ‘yan majalisa, ciki har da manyan mambobin majalisar tarayya zuwa APC.
Daga cikin ‘yan majalisar tarayya da suka bar tsohuwarsu zuwa APC akwai Sanata Agom Jarigbe daga Jihar Kuros Ribas da Sunday Marshal Katung daga Kaduna.
Tun daga shekarar 2023 har zuwa yanzu, jam’iyyun adawa a majalisar wakilai sun rasa akalla mambobi 66 zuwa jam’iyyar APC mai mulki.
Babbar jam’iyyar adawa ta PDP wadda ta rasa ‘yan majalisu 44, sai LP 14, NNPP 6, ADC 1 da YPP 1.
A lokacin da aka kaddamar da majalisar a watan Yuni 2023, tsarin majalisar wakilai ya kasance APC tana da kujeru 178, PDP 115, LP 35, NNPP 19, APGA 5, SDP 2, YPP 2 da ADC 2.
Bayan guguwar sauya sheka, yawan ‘yan majalisar yanzu sun kasance kamar haka: APC 246, PDP 71, LP 21, NNPP 13, APGA 5, SDP 2, ADC 1 da YPP 1.
A ranar Juma’a da ta gabata, mambobi 16 na majalisar dokokin Jihar Ribas karkashin jagorancin shugaban majalisan, Martin Amaewhule, sun sauya sheka daga PDP zuwa APC.
Lokacin da aka kaddamar da majalisar dokoki ta kasa ta 10 a ranar 13 ga Yunin 2023, jam’iyyar APC ta rike kujeru 59 a majalisar dattawa.
Amma jam’iyyar ta kara tumbatsa zuwa samu sanatoci 76, ta wuce kashi biyu bisa uku na samun rinjaye, bayan samun sauya sheka da ‘yan majalisar dattawan suka shiga cikinta.
Lokacin da aka amince da ADC a matsayin jam’iyyar hadaka ta tsofaffin shugabannin PDP, jam’iyyar ta sami sabon rayuwa tare da shigowar manyan mambobin PDP da suka hada da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da tsohon shugaban majalisar dattawa, Dabid Mark da tsohon gwamnan Jihar Osun, Rauf Aregbesola da wasu.
Yawan wadanda ke barin PDP suna shiga APC ne, yayin da kadan daga ciki suke shiga ADC.
Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir Elrufai ya sauya sheka daga APC zuwa SDP, sannan daga baya ya shiga ADC.
PDP ita ce kawai babbar jam’iyya da ba ta amfana daga guguwar sauyin sheka ba, amma tana ci gaba da rasa babban adadin mambobinta.
Wani masanin siyasa kuma farfesa a fannin kimiyyar siyasa, Gbade Ojo, wanda ya yi magana da wakilinmu kan wannan batu, ya lura cewa rushewar jam’iyyun adawa yana da babban tasiri wajen yawan tserewar mambobi, yana mai cewa hakan ya kara rage gwarin gwiwar al’ummar Nijeriya.
“Idan ka kalli majalisa, APC yanzu tana da gagarumi rinjaye a duka majalisar wakilai da majalisar dattawa. Ayyukan sa ido nasu suna da rauni sosai saboda shugaban kasa ya nada jami’an da su ne za su je su gudanar da ayyukan sa ido a kansu. Amma yawancinsu yanzu suna cikin jam’iyyar gwamnati,” in ji shi.
Sau da dama PDP ta yi kokari dawo da martabar jam’iyyar. Ta gudanar da babban taro a matakin gundumomi da karamar hukumomi da jihohi da dama kuma kasa baki daya, inda mambobi suka zabi sabon shugaban jam’iyyar na kasa.
Amma lamarin ya ci tura, inda magoya bayan ministan Abuja, Nyesom Wike suka kalubalantar babban taron.
Wasu na cewa ko da an gudanar da babban taron zaben, jam’iyyar ta kasa haifar da irin amincewar da zai sa mambobinta su ci gaba da kasancewa wuri guda.
Duk da yake akwai alamun da ke cewa ko wadanda suka saura na iya barin jam’iyyar a kowane lokaci.
Masana na cewa ci gaban rikicin a jam’iyyar da shari’o’i da dama na iya sanya ‘yan takararta a 2027 cikin hadari ta fuskar doka, musamman gwamnonin da ke neman wa’adi na biyu su nemi wasu jam’iyyar.
A hankali, ADC tana samun karuwa a matsayin babban jam’iyyar adawa a kasar, tana matsar da PDP zuwa baya, wacce ta rike wannan matsayi tun bayan ta fadi a zaben shugaban kasa a 2015, zuwa matsayi na biyu.
A kwanan nan, jam’iyyar ta ce tana shirin karbar sama da mambobin majalisar ta 10 guda 100 kafin zaben shekarar 2027.
A halin yanzu APC na da yawancin ‘yan majalisa a duka majalisun dokoki kasar nan tare da zargin cewa wasu na shirin shiga jam’iyyar.
Akwai rahotannin da ke cewa a jihohi kamar Benuwai, Kano, Adamawa da Yobe cewa ADC ta kafu kuma za ta bunkasa c
ikin ‘yan watanni kadan masu zuwa.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA