An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin
Published: 29th, October 2025 GMT
Kakakin ma’aikatar kula da muhalli ta kasar Sin Pei Xiaofei ya bayyana a yau cewa, yanayin ruwa da na iska a kasar ya ci gaba da ingantuwa a cikin watanni 9 na farkon bana.
A cewarsa, matsakaicin nauyin burbushin abubuwan dake cikin iska na PM2.5, wanda shi ne muhimmin ma’aunin gurbatar iska, ya tsaya kan microgram 26 kan kowane cubic mita, a cikin birane ko garuruwan Sin 339, daga watan Janairu zuwa na Satumba, wannan ya nuna cewa an samu raguwar ma’aunin da kaso 5.
Haka kuma, cikin watanni 9 na farkon bana, an samu ingantacciyar iska a kaso 87.6 na kwanakin, wanda ya karu da maki kaso 1.8 kan na bara.
Ma’aikatar ta kuma bayyana cewa a wannan lokaci, an kasa kaso 89 na matattarar ruwa 3,641 dake karkashin kulawar kasar Sin bisa matakin inganci daga 1 zuwa III, wanda ke nuna ingancinsu, wanda ya karu da kaso 0.5 kan na makamancin lokacin a bara. (Mai fassara: FMM)
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
Zanga-zanga ta ɓarke a Kamaru
Rahotonni sun bayyana ɓarkewar zanga-zanga a birnin Douala, cibiyar kasuwancin Kamaru jim kadan bayan sanar da sakamakon zaɓen shugaban ƙasar.
Wasu bidiyoyi da aka yaɗa a dandalan sada zumunta sun nuna gomman mutane sun fantsama kan titunan birnin, tare da rera waƙoƙin goyon bayan Issa Tchiroma Bakary, jagoran adawar ƙasar.
An rufe makarantu saboda ƙarancin man fetur a Mali Paul Biya mai shekara 92 ya lashe zaɓen KamaruKamfanin dillancin labaran Kamaru, ya wallafa wani bidiyo da ke nuna yadda aka lalata wani ginin majalisar birnin, bayan da masu zanga-zangar suka far masa.
BBC ya ruwaito cewa, a yayin da ake ci gaba da zaman ɗar-ɗar kan abin da ka iya faruwa bayan sanar da sakamakon zaɓen Kamaru, makarantu da shaguna sun kasance a rufe a Yaoundé, babban birnin ƙasar.
Hatta ma’aikatan gwamnati da dama sun ƙi fita wuraren ayyukansu saboda fargabar abin da ka iya biyo bayan sanar da sakamakon zaɓen.
Sai dai rahotanni sun nuna cewa girke jami’an tsaro masu yawa a manyan birane, musamman Yaoundé, Douala da kuma Garoua, mahaifar jagoran adawa Tchiroma Bakary, ya taƙaita zanga-zangar da aka fara gudanarwa.
Kawo yanzu, yawancin ‘yan ƙasar sun ci gaba da kasancewa a cikin gidajensu bayan da aka bayyana Shugaba Paul Biya a matsayin wanda ya lashe zaɓen, wanda hakan ke tabbatar masa da wa’adin mulki na takwas.
Shugaba Paul Biya shi aka sanar a hukumance a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa karo na takwas a cewar Kotun Tsarin Mulkin Kamaru, yayin da tun farko jagoran ’yan adawa Issa Tchiroma Bakary ya ayyana kansa a matsayin wanda ya yi nasara.