Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?
Published: 27th, October 2025 GMT
Sa’an nan matakin da kasar Sin ke dauka yanzu, shi ne jagorantar manyan gyare-gyare kan tsare-tsaren samar da kayayyaki na duniya, ta yadda ita da dukkan kasashe masu tasowa za su samu damar inganta tsare-tsarensu na tattalin arziki, musamman ma a bangaren masana’antu. Dangane da batun, babbar darektar hukumar kasuwanci ta duniya (WTO) Ngozi Okonjo-Iweala, ta bayyana a wajen taron dandalin tattaunawa na Abuja karo na 6, da ya gudana a kwanakin baya, cewa “Sauyawar tsare-tsaren samar da kayayyaki na duniya ta haifar da damammaki ga kasashen Afirka, ta fuskar janyo jari, da karfafa bangaren masana’antu.
Hakika, ma iya cewa maganar Madam Ngozi ta riga ta zama gaskiya, ta yin la’akari da yadda kasar Sin take zuba jari da raya masana’antu a kasashen Afirka daban daban. Sai dai ci gaban masana’antun kasashen Afirka da Sin suna haifar da sauyawar yanayi kan tsohon tsarin tattalin arzikin duniya. Hakan ya sa kafofin yada labarai na kasashen yamma suka dinga yada jita-jita game da kasar Sin, da hadin gwiwarta da kasashen Afirka. To, abun da ya kamata kasashen Afirka da kasar Sin su yi, shi ne rufe kunnuwansu, da kokarin neman ci gaban tattalin arziki, da gina wata duniya mai adalci da samun daidaito. (Bello Wang)
ShareTweetSendShare MASU ALAKAকীওয়ার্ড: da kasar Sin
এছাড়াও পড়ুন:
Mata Ne Ginshikin Ci-Gaban Al’umma – Gimbiyar Dange
Gwamnan Jihar Sokoto, Ahmad Aliyu, wanda Kwamishinan Ruwa, Alhaji Aminu Dodo Iya, ya wakilta, ya jaddada cewa sarautun gargajiya su ne ginshiƙin zaman lafiya da ci-gaban al’umma. Ya ce shugabannin gargajiya na taka rawa wajen haɗa kan jama’a da gwamnati, tare da tabbatar da ɗorewar cigaba a matakin jiha da ƙasa baki ɗaya.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA