Wilayati: Kasashen Ian, China Da Rasha Suna Taka Rawa A Fagen Kafa Sabon Tsarin Duniya
Published: 28th, October 2025 GMT
Mai bai wa jagoran juyin musulunci na Iran shawara akan harkokin siyasar kasa da kasa Dr. Ali Akbar Wilayati ya ce; Da akwai kasashe uku a cikin Asiya wadanda suke da ‘yanci da su ne Iran, China da Rasha, kuma suna taka rawa domin samar da sabon tsarin tafiyar da duniya.
Dr. Wilayati ya bayyana hakan ne dai a yayin ganawarsa da jakadan China a Iran “Zong Bi Wuu” yana mai kara da cewa; Alaka a tsakanin kasashen biyu ta dade da kuma zurfi.
Har ila yau Wilayati ya ce alakar kasashen biyu ta ginu ne akan maslaha da kuma girmama juna da kuma cin gashin kai na siyasa, da hakan ya mayar da su, tare da kasar Rasha zama kasashen Asiya uku masu ‘yanci.
Haka nan kuma Wilayati yay aba wa matsayar da kasar China take dauka akan Iran,musamman dangane da batun takunkumin wanda ya ce, yana nuni da yadda Beijing take taka rawa a fagen siyasar duniya.
A nashi gefen, jakadan kasar ta China a Iran Zong Bi Wuu ya bayyan jin dadinsa akan ganawarsa da Ali Akbar Wilayati, tare da kuma bayyana yadda alaka tare a tsakanin kasarsa da Iran a lokaci mai tsawo.
Haka nan kuma ya ce, kasarsa China tana bayar da muhimmanci ga alakarta da Iran , haka nan kuma ya yi godiya jagoran juyin musulunci da yake bai wa alaka da China muhimmanci.
Bangarorin biyu sun kuma tattaunawa abubuwan da suke faruwa a fagen siyasar kasa da kasa da kuma a cikin wannan yankin na yammacin Asiya.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Zaben Ivory Coast: Alassane Ouattara na kan gaba da tazara mai yawa October 27, 2025 Pezeshkian: Hadin kan Musulmi zai iya dakile zalincin kasashen waje October 27, 2025 Amurka ta tsare wani dan jarida musulmi saboda sukar Isra’ila October 27, 2025 Kashi 84% na ‘yan Faransa ba su gamsu da Macron ba a matsayin Shugaba October 27, 2025 Iran ta bukaci MDD ta nisanci nuna bangaranci game da masu keta dokokin duniya October 27, 2025 Kamaru : Paul Biya, ya lashe zaben shugaban kasar a karo na takwas October 27, 2025 An Nada Birgediya Janar Qarshi A Matsayin Mataimakin Babban Kwamandan Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci October 27, 2025 Hamas Ta Ce: Kungiyar Ta Ba Da ‘Yanci Ga Masu Shiga Tsakani Zabar Membobin Kwamitin Gudanar Da Gaza October 27, 2025 Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kashe ‘Yan kasar Lebanon Biyu Tare Da Jikkatan Wasu Biyu Na Daban October 27, 2025 Amnesty International Ta Bukaci Bayyana Makomar Masu Fafutukar Kare Hakkin Bil’Adama Da Suka Bace A Uganda October 27, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Wilayati ya
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Gudanar Da Taro Kan Yadda Manzon Allah (s) Ya Yi Mu’amala Da Wadanda Ba Musulmi Ba
Ana taro kan yadda manzon Allah mohammad dan Abdullahi (a) ya zauna da wadanda ba musulmi ba a rayuwarsa a Madina.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto hukuma mai kula da al-adu da kuma al-amuran addinin Musulunci a nan Iran tana cewa ana gudanar da wannan taron ne a dai dai lokacinda aka fara bukukuwan cika shekaru 1500 na hijirar manzon Allah (s).
Labarin ya kara da cewa an sabi baki wadanda suka gabatar da jawabi masu muhimmanci daga kasashen Iran, Lebanon da kuma Masar.
Ahmad Mobaleghi na mamba a kwamitin al-amuran addini na hukumar ya kawo ayoyin al-kur’ani wadanda suka yi mgana kan yadda manzon Allah yayi mu’amala da yahudawan da ya samu a Madina, kuma ya ce wadannan ayoyi kekyawar misali ne nazamantakewar Musulmi da wadanda ba musulmi ba.
Louis Saliba wani marubu ce kirista daga kasar Lebanon, wanda kuma ya gabatar da Jawabinsa ta kafar Bidiyo daga kasar Lebanon yay aba da yadda manzon Allah (s) yayi mu’amala da nasaran Najran wadanda suka zo masa daga kasar yemen.
Sai kuma Abdolsalam Emami, mai bawa ma’aikatar al-adu shawara kan mabiya mazhabar sunna a nan Iran yayi magana a kan yadda manzon Allah (s) ya zauna da yahudawa a Madina ya kuma kawo misalai da dama wadanda suka shafi hakan.
Sai kuma Amani Mahmoud Ibrahim, sheikhin malami a Jami’ar Al-Azhar ta kasar Masar wanda ya kawo yadda yahudawan Madina suka saba al-kawalin da suka cimma da manzon Allah (s) a farkon hijira da kuma yadda yayi mu’amala da su.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Najeriya: Jirgin Sojojin Kasar Yana Kan Hanyarsa Ta Zuwa Portugal, Amma Ta Sauka A Burkina Faso December 9, 2025 Saudiya da Qatar Zasu Gina Layin Dogo Mai Sauri Tsakanin Kasashen Biyu December 9, 2025 Nigeria Ta Aike Da Jiragen Yaki Zuwa Kasar Benin Domin Dakile Yunkurin Juyin Mulki December 9, 2025 Pakistan ta Bai Wa Taliban Ta Aghanistan Zabi A Tsakanin Mu’amala Da Ita Ko Da ‘Yan Ta’adda December 9, 2025 Kasashen Iran Da Turkiya Za Su Bunkasa Alakarsu A Fagen Ilimi Da Musayar Fasaha December 9, 2025 An Fito Da Gawawwakin Shahidai 98 Da Aka Binne Cikin Gaggawa A Asibitin “Ash-Shifa” December 9, 2025 Talauci Yana Karuwa A “Isra’ila” Bayan 7 Ga Watan Oktoba December 9, 2025 AU Ta yi Tir Da Harin RSF A Makarantar Kananan Yara Da Ya Kashe Mutane 80 December 8, 2025 MِِِِDD: Kisan Kare Dangin Da Isra’ila Ta yi A Gaza Shi Ne Farko Da Yafi Jan Hankalin duniya December 8, 2025 Iran Da Azarbaijan Sun Amince Da Ci Gaba Da Tuntubar Juna Domin Warware Matsaloli December 8, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci