Mai bai wa jagoran juyin musulunci na Iran shawara akan harkokin siyasar kasa da kasa Dr.  Ali Akbar Wilayati ya ce; Da akwai kasashe uku a cikin Asiya wadanda suke da ‘yanci da su ne Iran, China da Rasha, kuma suna taka rawa domin samar da sabon tsarin tafiyar da duniya.

Dr. Wilayati ya bayyana hakan ne dai a yayin ganawarsa da jakadan China a Iran “Zong Bi Wuu” yana mai kara da cewa; Alaka a tsakanin kasashen biyu ta dade da kuma zurfi.

 Har ila yau Wilayati ya ce alakar kasashen biyu ta ginu ne akan maslaha da kuma girmama juna da kuma cin gashin kai na siyasa, da hakan ya mayar da su, tare da kasar Rasha zama kasashen Asiya uku masu ‘yanci.

Haka nan kuma Wilayati yay aba wa matsayar da kasar China take dauka akan Iran,musamman dangane da batun takunkumin wanda ya ce, yana nuni da yadda Beijing take taka rawa a fagen siyasar duniya.

A nashi gefen, jakadan kasar ta China a Iran Zong Bi Wuu ya bayyan jin dadinsa akan ganawarsa da Ali Akbar Wilayati,  tare da kuma bayyana yadda alaka tare a tsakanin kasarsa da Iran a lokaci mai tsawo.

Haka nan kuma ya ce, kasarsa China tana bayar da muhimmanci ga alakarta da Iran , haka nan kuma ya yi godiya jagoran juyin musulunci da yake bai wa alaka da China muhimmanci.

Bangarorin biyu sun kuma tattaunawa abubuwan da suke faruwa a fagen siyasar kasa da kasa da kuma a cikin wannan yankin na yammacin Asiya.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Zaben Ivory Coast: Alassane Ouattara na kan gaba da tazara mai yawa October 27, 2025 Pezeshkian: Hadin kan Musulmi zai iya dakile zalincin kasashen waje October 27, 2025 Amurka ta tsare wani dan jarida musulmi saboda sukar Isra’ila October 27, 2025 Kashi 84% na ‘yan Faransa ba su gamsu da Macron ba a matsayin Shugaba October 27, 2025 Iran ta bukaci MDD ta nisanci nuna bangaranci game da masu keta dokokin duniya   October 27, 2025 Kamaru : Paul Biya, ya lashe zaben shugaban kasar a karo na takwas October 27, 2025 An Nada Birgediya Janar Qarshi A Matsayin Mataimakin Babban Kwamandan Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci   October 27, 2025 Hamas Ta Ce: Kungiyar Ta Ba Da ‘Yanci Ga Masu Shiga Tsakani Zabar Membobin Kwamitin Gudanar Da Gaza October 27, 2025 Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kashe ‘Yan kasar Lebanon Biyu Tare Da Jikkatan Wasu Biyu Na Daban October 27, 2025 Amnesty International Ta Bukaci Bayyana Makomar Masu Fafutukar Kare Hakkin Bil’Adama Da Suka Bace A Uganda   October 27, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Wilayati ya

এছাড়াও পড়ুন:

Kasashen ECOWAS sun rage kudin sufirin jiragan sama a tsakaninsu  

Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) ta amince da wasu sauye-sauye da nufin rage tsadar tafiye-tafiyen jiragen sama a tsakanin kasashe mambobin kungiyar.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Laraba, Hukumar ECOWAS ta sanar da cewa shugabannin kasashe da gwamnatoci, a taronsu a Abuja, sun amince da wata manufa ta kawar da harajin sufurin jiragen sama da kuma rage kudin tikitan jirgin sama da kashi 25 cikin 100, wanda zai fara aiki daga ranar 1 ga Janairu, 2026.

Hukumar ta bayyana cewa wannan matakin ya biyo bayan shekaru da dama na koma baya a fannin sufurin jiragen sama a Yammacin Afirka, galibi saboda yawan haraji, wanda ke hana bukatar tafiye-tafiye da kuma raunana jarin da ake zubawa a fannin tafiye tafiye na jiragen sama.

Nazarin da ECOWAS da Tarayyar Afirka, da Kungiyar Jiragen Sama ta Afirka (AFRAA), da Kungiyar Sufurin Jiragen Sama ta Duniya (IATA) suka gudanar sun nuna cewa Yammacin Afirka ya kasance daya daga cikin yankuna mafi tsada don tafiye-tafiyen jiragen sama, inda fasinjoji wani lokacin ke biyan har zuwa caji 66 daban-daban, yayin da kamfanonin jiragen sama ke fuskantar kudade daban-daban.

ECOWAS ta yi gargadin cewa hauhawar farashin jiragen sama na hana tafiye-tafiyen fasinjoji, rage yawan yawon bude ido, kawo cikas ga ciniki, da kuma lalata ajandarta ta ‘yancin zirga-zirga da hadewar yankuna.

A cewar sanarwar, amincewa da Dokar na da nufin magance wadannan kalubalen da kuma daidaita yankin da ka’idojin jiragen sama na duniya.

Kungiyar ta jaddada cewa ya kamata wadannan gyare-gyare su taimaka wajen rage farashin tikiti, kara yawan fasinjoji, karfafa kamfanonin jiragen sama na yankin, bunkasa ayyukan filayen jiragen sama da kuma samar da karin damammaki na tattalin arziki ga al’ummomin da ke karbar bakuncin.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Dakarun IRGC 3 Sun Yi Shahada A wani Harin Ta’addanci A Kudancin Kasar Iran December 11, 2025 Hamas: HKI Tana Ci Gaba Da Keta Bangaren Farko Na Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza December 11, 2025 Iran Ta Yi Tir Da Yanke Tallafin Da MDD Take Bawa Yan Gudun Hijiran Afganistan December 11, 2025 Ansarallah: Dole Ne Kasar Yemen Ta Tsarin Musulunci Na Kaiwa Ga Daukaka December 11, 2025 Shugaban Iran Ya Isa Astana Babban Birnin Kazakhstan December 11, 2025 ECOWAS ta bukaci waware batutuwa na siyasa ta hanyoyin lumana a yammacin Afirka December 11, 2025 Reuters: Amurka na matsa lamba kan kotun ICC don janye bincike kan yakin  Gaza da Afghanistan December 11, 2025 Ghana ta yi Allah wadai da cin mutuncin ‘yan kasarta da ke balaguro a Isra’ila December 11, 2025 Sakamkon Jin Ra’ayi: Yawancin Amurkawa na adawa da kai hari kan Venezuela December 11, 2025 Hamas Ta yi Tir Da Sabbin Matsugunan Yahudawa Da Isra’ila Ke yi A Yankunan Da Ta Mamaye December 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Pezeshkian: Duniya Tana Bukatar Amintaccen Madogara, Zaman Lafiya Da Kuma Hadin Kai
  • Iran Zata Dauki Bakoncin Taro Dangane Da Kasar Afganistan Da Tsaron Yankin
  • Kasashen ECOWAS sun rage kudin sufirin jiragan sama a tsakaninsu  
  • Ansarallah: Dole Ne Kasar Yemen Ta Tsarin Musulunci Na Kaiwa Ga Daukaka
  • Sakamkon Jin Ra’ayi: Yawancin Amurkawa suna adawa da yunkurin kai hari kan Venezuela
  • Kasashen Nijeriya Da Saudiyya Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Tsaro Ta Shekaru 5 
  • Iran Ta yi Tir Da Kisan Karen Dangin Isra’ila A Gaza A Ranar Yaki Da Kisan Kiyashi Ta MDD
  • Iran Tana Daukar Bakwancin Taron BRICS Na Binciken Kimiya Da Kuma Ci Gaban Ilmi
  • Nasarar Da Iran Ta Samu A Yakin Kwanaki 12 Kan HKI Yana Jawo Hankalin Kasashen Duniya
  • Ganawa A Tsakanin Mataimakan Ministocin Waje Na Kasashen Saudiyya, China Da Minista Arakci Na Iran