Babban daraktan hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa Rafael Grossi ya sanar da shirin kai ziyara birnin Tehran nan da makwanni masu zuwa a yayin da ake ci gaba da tattaunawa don tsaida takamaimen lokacin.

Ziyarar ta zo ne a wani bangare na ci gaba da huldar diflomasiyya tsakanin Iran da hukumar IAEA, da nufin tinkarar batutuwan da suka shafi Nukiliya, da samar da hadin gwiwar fasaha cikin tsarin alkawurran da Iran ta dauka a karkashin yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya (NPT).

Ziyarar ta kuma jaddada irin hadin gwiwar da Tehran ke ci gaba da yi da hukumar ta IAEA, duk da matsin lamba daga waje da kuma zargin siyasa daga kasashen yammacin Turai.

Da yake amsa tambaya daga wakilin TASS, Grossi ya tabbatar da cewa ana tattaunawa don tsara ziyararsa a makonni masu zuwa.

Wannan bai ta ce ziyarar Rafael Grossi, t afarko a Iran ba, don kuwa ko a kasrhen  watan Nuwamban bara ya gana da shugaban Iran Masoud Pezeshkian da ziyarce-ziyarcen cibiyoyin nukiliya na Fordow da Natanz.

Ziyarar Grossi ta zo ne a daidai lokacin da Iran ke ci gaba da tabbatar da hakkinta na samar da makamashin nukiliya cikin lumana karkashin dokokin kasa da kasa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Wike ya rufe ofishin FIRS da Bankin Access kan rashin biyan haraji

Hukumar Kula da Babban Birnin (FCTA) Tarayya ta rufe ofishin Hukumar Tara Haraji ta Kasa (FIRS) da kuma ginin Bankin Access kan rashin biyan haraji na sama da shekaru 25.

Daraktan Kula da Filaye na Hukumar FCTA, Chijioke Nwankwoeze, ya bayyana cewa hukumar bin ginin da bankin Access yake bashin harajin shekara 35, ofishin FIRS da ke unguwar Wuse Zone 5 kuma bashin harajin shekara 25.

Babban Ofishin na FIRS na daga cikin fitattun gine-gine da Hukumar Tara Kuɗaɗen Haraji na Babban Birnin ta rufe a safiyar Litinin, kan zargin rashin biyan haraji.

Sauran sun  shafa da ginin Bankin Access da da ofishin kamfanin mai Total Energy da fitaccen otel din Ibro Hotel a unguwar Wuse, da sauran wurare 4,700 a Abuja.

Rikici ya barke a taron Atiku da kungiyoyin Arewa NAJERIYA A YAU: Tasirin Dangantakar Bangaren Zartarwa Da Na Majalisa A Kan Talaka

Chijioke Nwankwoeze, ya bayyana cewa ginin bankin Access da matakin ya shafa, mallakin wani wani kamfani ne, inda bankin ta kama haya.

Kazalika hukumar ta kwace izinin mallakar wasu filaye a wasu fitattun unguwanni saboda matsalar rashin biyar harajin.

Daraktan Kula da Bunƙasa Birnin Abuja, Mukhtar Galadima, ya jagoranci aikin ne bayan hukumar ta fitar da sanarwar rashin biyan harajin da ya kamata.

Ya bayyana cewa ana bin kamfanin Total harajin Shekara 10, wanda ya cika a watan Maris na 2025.

Fili mai lamba 2456 da ke titin Cadastral Zone A02, a unguwar Maitama, mallakin Kamfanin Rana Taher Furniture saboda rashin biyan harajin kas ana shekara 34.

Galadima ya bayyana cewa aikin zai ci gaba a sauran unguwannin Abuja, yana mai gargaɗin waɗanda abin ya shafa su gaggauta yin abin da aya kamata, ko su kuka da kansu.

Hukumar FCDA ta tsaurara matakan karbar haraji, musamman kam dokokin da suka shafi gine-gine da mallakar kasa a ƙarƙashin Minista mai ci, Barista Nyesom Wike.

Ya bayyana cewa wajibi ne masu filayen da hukumar ta kwace su tashi nan take, su bi hanyar da ta dace domin warware duk wata matsala.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Arakci: Idan Birtaniya Ta Ci Gaba Da Batun Dakatar Da Tace Uranium A Iran, Za A Dakatar Da Tattaunawa Da Ita
  • Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Kasa Na Yara Jagorori Na Kasar Sin 
  • CMG Ta Cimma Nasarar Gudanar Da Gasar Mutum-Mutumin Inji Ta Kasa Da Kasa
  • Firaministan Pakistan na ziyara Tehran mai manufar inganta dangantaka tsakanin kasashen biyu
  • Kwastam ta kama Tiramol ta N150m, ta miƙa wa NAFDAC a Kano
  • Wike ya rufe ofishin FIRS da Bankin Access kan rashin biyan haraji
  • Mene Ne Dalilin Amurka Na Cewa Zata Harba Makamamin Nukiliya Kan Yankin Zirin Gaza?
  • Ruhin Yuan Longping Ya Ba Da Tabbaci Ga Samar Da Isashen Hatsi a Nahiyar Afirka
  • Gasar Wasanni Ta Kasa: Jihar Binuwai Ta Samu Kyaututtuka 9 Zuwa Yanzu
  • An Kaddamar Da Babban Filin Wasan Da Kasar Sin Ta Gina Wa Kasar Chadi Kyauta