Babban daraktan hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa Rafael Grossi ya sanar da shirin kai ziyara birnin Tehran nan da makwanni masu zuwa a yayin da ake ci gaba da tattaunawa don tsaida takamaimen lokacin.

Ziyarar ta zo ne a wani bangare na ci gaba da huldar diflomasiyya tsakanin Iran da hukumar IAEA, da nufin tinkarar batutuwan da suka shafi Nukiliya, da samar da hadin gwiwar fasaha cikin tsarin alkawurran da Iran ta dauka a karkashin yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya (NPT).

Ziyarar ta kuma jaddada irin hadin gwiwar da Tehran ke ci gaba da yi da hukumar ta IAEA, duk da matsin lamba daga waje da kuma zargin siyasa daga kasashen yammacin Turai.

Da yake amsa tambaya daga wakilin TASS, Grossi ya tabbatar da cewa ana tattaunawa don tsara ziyararsa a makonni masu zuwa.

Wannan bai ta ce ziyarar Rafael Grossi, t afarko a Iran ba, don kuwa ko a kasrhen  watan Nuwamban bara ya gana da shugaban Iran Masoud Pezeshkian da ziyarce-ziyarcen cibiyoyin nukiliya na Fordow da Natanz.

Ziyarar Grossi ta zo ne a daidai lokacin da Iran ke ci gaba da tabbatar da hakkinta na samar da makamashin nukiliya cikin lumana karkashin dokokin kasa da kasa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya dawo Najeriya bayan ziyarar aiki a Saint Lucia da Brazil

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya dawo gida Najeriya bayan kwashe makonni biyu, inda ya ziyarci ƙasashen Saint Lucia da Brazil.

Mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga, ne ya sanar da hakan a shafinsa na X.

Sanatan Abuja ta sauya sheƙa zuwa ADC Abin da ya faru tsakani na da DSS bayan kama ni — Ɗan Bello

Shugaba Tinubu ya bar Najeriya ne a ranar 28 ga watan Yuni, 2025 don ziyarar aiki a waɗannan ƙasashe biyu.

Da farko ya je Saint Lucia domin ƙarfafa dangantaka tsakanin Najeriya da ƙasashen yankin Caribbean, da kuma ƙara haɗin gwiwa tsakanin ƙasashen kudancin duniya.

A ranar 4 ga watan Yuli, Tinubu ya tashi daga Saint Lucia zuwa Brazil, inda ya halarci taron BRICS na shekarar 2025, wanda aka gudanar daga 6 zuwa 7 ga watan Yuli, 2025.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya dawo Najeriya bayan ziyarar aiki a Saint Lucia da Brazil
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce; An Mika Batun Hakin Gwiwa Tsakanin Iran Da Hukumar IAEA Ga Kwamitin Kolin Tsaron Kasa
  • Magance Matsalar Yara Da Ba Sa Zuwa Makaranta: Gwamnan Zamfara Ya Ƙaddamar Da Shirin Ciyarwa A Makarantun Jihar
  • Gwamnan Zamfara Ya Raba Buhunan Taki 59,205 Ga Manoman Jihar
  • Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista
  • NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta
  • Shugaban Kasar Iran Yace Huldar kasar Iran Da IAEA Zai Ci Gaba Ne Idan Ta Daina Fuska Biyu
  • Majalisar Limaman Turai Ta Nesanta Kanta Daga Wadanda Su Ka Ziyarci HKI
  • Dangote Ya Yaba Wa Tinubu Kan Samar Da Ababen More Rayuwa A Nijeriya
  • Kwamandan Sojin Iran Ya Jaddada Kare Kan Iyakokin Jamhuriyar Musulunci Ta Iran