Aminiya:
2025-05-01@00:31:15 GMT

Gwamnonin PDP sun garzaya Kotun Ƙoli kan dakatar da Gwamnan Ribas

Published: 24th, March 2025 GMT

Wasu daga cikin gwamnonin jam’iyyar adawa ta PDP sun maka Shugaba Bola Tinubu a Kotun Ƙoli kan dakatar da Gwamnan Ribas, Similanayi Fubara.

Gwamnonin sun garzaya kotun ne domin neman fatawa game da abin da sashe na 305 na kundin mulkin ƙasar ke nufi.

Ban bai wa majalisa haƙuri ba — Natasha Juventus za ta sallami kocinta Thiago Motta

Gwamnonin da ke kan gaba a shigar da ƙarar sun haɗa da na jihohin Adamawa, Bauchi, Bayelsa, Enugu, Osun, Filato, Zamfara.

Daga cikin abubuwan da suke nema akwai neman kotun ta ɗauki matsaya kan ko sashen na 305 na kudin mulkin Nijeriya na 1999 ya bai wa shugaban ƙasa dama ya dakatar da zaɓaɓɓen gwamna da mataimakiyarsa da majalisar dokoki ta jiha, kuma ya naɗa wani gwamnan riƙo a ƙarƙashin dokar ta-ɓaci.

A ƙunshin takardun da suka gabatar wa kotun, gwamnonin sun ce dakatar da zaɓaɓɓun shugabanni da Shugaba Tinubu ya yi na cin karo da sassa na 1(2) da na 5(2) da kuma na 305 da ke ƙunshe a Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya.

Matakin na zuwa bayan huɗu cikin shida na gwamnonin yankin kudu maso kudu sun yi tir da dokar da Tinubu ya ayyana a Ribas.

Gwamnan Bayelsa Duoye Diri, wanda shi ne shugaban ƙungiyar gwamnonin yankin, ya ce, “rikicin siyasar na Ribas bai kai abin da za a ayyana dokar ta-ɓaci a kai ba kamar yadda sashe na 305(3) ya tanada.”

Sai dai kuma, gwamnonin Edo da na Kuros Riba sun goyi bayan matakin na Shugaba Tinubu.

A gefe guda kuma, ƙungiyar neman shugabanci na gari ta Socio-Economic Rights and Accountability Project (Serap) ta ce ta shigar da Tinubu ƙara a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja game da dakatar da gwamnan Ribas da mataimakiyarsa da majalisar dokoki “wanda ya saɓa wa doka”.

Ana iya tuna cewa, a ranar 18 ga wannan wata na Maris ne Tinubu ya dakatar da Gwamna Similanayi Fubara da mataimakiyarsa, Ngozi Odu da duk ’yan majalisar dokokin Jihar Ribas na tsawon watanni shida tare da ɗora tsohon Babban Hafsan Sojin Ruwa, Rear Admiral Ibok-Ete Ibas a matsayin kamtoman jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamnoni Siminalayi Fubara

এছাড়াও পড়ুন:

Wang Yi: Neman Sulhu Da Ja Da Baya Riba Ne Ga Masu Son Cin Zali

Ministan harkokin wajen kasar Brazil Mauro Vieira ne ya jagoranci wannan taro, inda bangarori daban daban suka tattaunawa kan yadda kasashen BRICS za su karfafa zaman lafiya da tsaron duniya. (Mai Fassara: Maryam Yang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnan Sokoto Ya Amince Da Sauya Wa Manyan Sakatarori 25 Ma’aikatu A Jihar 
  • Tinubu zai ziyarci Katsina
  • Saudiya Ta Yi Allawadai Da Kissan Kiyashin Da HKI Take Yi A Gaza A Gaban Kutun ICJ
  • Wang Yi: Neman Sulhu Da Ja Da Baya Riba Ne Ga Masu Son Cin Zali
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Sabon Firaiministan Kanada Mark Carney Murna
  • Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara 
  • Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa
  • Kotu Ta Kori Ƙarar Neman Diyyar N1bn A Kan Buhari Da Emefiele Kan Sauya Fasalin Naira
  • Shugaban Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Musulunci a Najeriya ya rasu
  • Takht Ravanji: Iran Ba Za Ta Taba Yin Tattaunawa Akan Dakatar Da Tace Sanadarin Uranium Ba