Iran Ta Bukaci Hukumar IAEA Ta Bayyana Matsayinta A Shirin Makamashin Nukliya Na Kasar
Published: 2nd, April 2025 GMT
A wata tattaunawa ta wayar tarho da shugaban hukumar makamashin Nukliya ta duniya Rafael Grossy Abbas Aragchi ministan harkokin wajen kasar Iran ya bukaci hukumar ta bayyana matsayinta dangane da shirin makamashin nukliyar kasar Iran.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ta nakalto ministan yana fadawa Grossy bayyana matsayin hukumarsa dangane da shirin nukliyar kasar Iran ta zaman lafiya, mai yuwa yayi tasiri a barazanar da kasar Iran take fuskanta na kai hare-hare kan cibiyoyin nukliyar kasar.
Aragchi ya kara jaddada cewa shirin Nukliyar kasar Iran na zaman lafiya ne, kuma har yanzun kasar Iran tana kan bakanta na aiki tare da hukumar makamashin nukliya ta duniya don kare hakkinta na mallakar fasahar makamashin nukliya wannan dokokin kasa da kasa duka bada.
Ministan ya bukaci hukumar , a irin wannan halin da Iran take ciki na fuskantar barazana ga cibiyoyinta na makamashin nukliya, akwai bukatar kwarai da gaske ga hukumar ta IAEA ta fito fili ta bayyana matsayinta.
A nashi bangaren babban daraktan hukumar makamashin nukliya ta duniya, Rafael Gorossy ya ce a shirye yake ya shiga tsakanin bangarorin biyu don tattaunawa da kuma fahintar juna kan wannan matsalar.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: makamashin nukliya kasar Iran ta
এছাড়াও পড়ুন:
Mutanen Sweida Na Kasar Siriya Suna Fama da Rashin Abinci da Ruwa
A yankin sweida na kudancin kasar Siriya mazauna wurin sun bayyana cewa abinci da ruwa da kuma kayakin bukatu nay au da kullum sun fara karanci sosai a yankin saboda yakin makonni uku da suke fafatawa da sojojin sabuwar gwamnati a Damascus.
Jaridar The National ta Amurka ta bayyana cewa yankin sweida na kudancin kasar Siriya wanda kuma HKI ta dade tana shigowa yankin ta fita a halin nyanzu yana fama da karancin abinci da ruwansha. Sannan da alamun har yanzun sojojin sabuwar gwamnatin kasar Siriya tana ci gaba da hana shigowar abinci da ruwa yankin duk tare da shelanta tsagaita wuta da aka yi.
Labarin ya kara da cewa. an kashe daruruwan mutane a fafatawar da mayakan hTI suka yi da drsawa da suka fi rinjaye a yankin da kuma wasu kananan kabilu a yankin.
Tun lokacinda HKI tare da taimakin kasashen turkiya da sauran kasashen yamma suka kifar da gwamnatin Bashar al-asad, kasar Siriya take fama da karin kashe-kashe na kabilanci da na addini a kasar.