Arakci: Babu Wanda Zai Yi Tunanin Kawo Wa Iran Hari
Published: 24th, March 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa; Iran tana cikin shirin ko-ta-kwana akan duk wani abu da zai iya bijirowa, kuma a halin yanzu ba batun yaki ake yi ba.
A wata ganawa da ministan harkokin wajen na Iran ya yi da tawagar kungiyar agaji ta “Red Cross” a karkashin jagorancin shugabanta Koliband, ministan harkokin wajen na Iran ya yabawa aikin nasu, tare da cewa; Duk da cewa ana cikin lokacin hutu, amma su a kodayaushe suna cikin shirin ko-ta-kwana domin gabatar da ayyukan agaji da hakan yake nuni da yi wa al’umma hidima ta koli.
Ministan harkokin wajen na Jamhuriyar Musulunci ta Iran Abbas Arakci ya kuma ce: Su ma sojoji da jami’an tsaro kamar ku suke aiki, ba su da lokacin hutu,kodayaushe suna cikin shirin ko-ta-kwana.
Haka nan kuma ya kara da cewa; Kowane bangare na gwamnati yana cikin shirin ko-ta-kwana domin fuskantar kowane irin yanayi.
Har ila yau, babban jami’in diflomasiyyar ta Iran ya ce; Ina da tabbacin cewa babu wani mahaluki da yake tunanin kawo wa Iran hari, domin suna sane da sakamakon da take tattare da yin hakan, sun kuma san cewa kowane bangare na gwamnati yana cikin shiri.
Abbas Arakci ya kuma bayyana cewa baya ga ayyukan agaji da kungiyar take yi a cikin gida, tana kuma gabatar da wasu ayyukan na taimako a kasashen waje. Ya kuma yi ishara da lokacin girgizar kasar Japan, da hukumar agaji ta Iran ta kai dauki, wanda ya taka rawa wajen kara bunkasa alaka a tsakanin kasashen biyu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe mafarauta 10 a Adamawa
Aƙalla wasu mutum 10 mafarauta sun rasa rayukansu yayin aikin ceto a ƙauyen Kopire da ke Ƙaramar Hukumar Hong ta Jihar Adamawa.
Shugaban ƙungiyar mafarautan Nijeriya reshen Arewa maso Gabas, Shawulu Yohanna ne ya tabbatar wa Aminiya hakan a ranar Talata.
Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno An dawo da wutar lantarki a Sifaniya da PortugalA cewarsa, ajali ya katse hanzarin mafarautan ne yayin wani arbatu da mayaƙan Boko Haram da suka yi musu kwanton ɓauna a jeji.
Ya bayyana cewa, mafarautan sun tunkari maharan ne bayan samun bayanan sirri da ke nuna cewa suna shirin kai hari.
“Abin takaicin shi yadda ake yi wa Gwamnan Borno ƙafar ungulu a ƙoƙarin da yake yi na ganin an kawo ƙarshen wannan hare-hare a yankin,” in ji shi.
Yohanna ya bayyana damuwa kan yadda mayaƙan Boko Haram ke ci gaba da ƙara ƙarfi a bayan nan da ke zama abin fargaba ga mazauna yankunan da abin ya shafa.
“Mun samu labarin cewa wani jirgi mai saukar ungulu ne yake jigilar mayaƙan daga sansaninsu zuwa wuraren da suke sheƙe ayarsu ba tare fuskantar wata tirjiya ba.
“Amma ina mai tabbatar da cewa muddin Gwamnatin Tarayya ta ɗauki mataki ta hanyar tanadar makamai na zamani, za a kawo ƙarshen waɗannan maƙiya cikin lokacin ƙanƙani.”
Ya roƙi Gwamnatin Tarayya da ta tanadar wa mafarauta da ’yan sa-kai manyan makamai na zamani domin kawo ƙarshen mayaƙan Boko Haram a yankin.
Wannan harin dai na zuwa ne ƙasa da sa’o’i 12 da wasu ’yan ta’adda suka kashe fiye da mutum 30 ciki har da mata da ƙananan yara a ƙananan hukumomin Kala Balge da Gambarou Ngala da ke jihar.