Neman “’Yancin Kan Taiwan” Da Jam’iyyar DPP Ke Yi Zai Ci Tura
Published: 2nd, April 2025 GMT
Tun daga ranar 1 ga watan Afrilu, dakarun rundunar sojojin ’yantar da al’umma ta kasar Sin ko PLA shiyyar gabashin kasar ta kaddamar da atisayen hadin gwiwar rukunoni masu kunshe da sojojin kasa, da na ruwa, da na sama da dai sauransu a kewayen tsibirin Taiwan. Atisayen da ya kasance wani salo na jan kunne mai karfi ga mahukuntan gwamnatin Lai Ching-te dake rajin “’yancin kan Taiwan”, kana mataki mai karfi da ya wajaba na kare ikon mulkin kai da cikakkun yankunan kasar Sin.
Kamar yadda aka sani, Taiwan wani sashe ne na kasar Sin, wanda ba ta taba zama kasa ba, kuma ba zai taba zama ba a nan gaba. Sunan yankin Taiwa a MDD shi ne “Lardin Taiwan na kasar Sin”. Duk yunkurin Lai Ching-te ba zai iya canza gaskiyar ba.
A daya hannun, matakin da babban yankin kasar Sin ya dauka ya nunawa kasashen duniya tsayayyiyar niyyar kasar ta tabbatar da nasarar warware batun Taiwan, da cimma manufar dinke dukkanin sassan kasar yadda ya kamata, kana ba za ta taba amincewa da duk wasu rukunoni ko mutanen dake neman balle Taiwan daga kasar Sin ba. Kowane karin girman kai da mahukuntan gwamnatin Lai Ching-te dake rajin “’yancin kan Taiwan” suka yi, za a bi shi da hukunci mai karfi daga babban yankin kasar Sin, kuma karshensu zai zo da wuri. (Mai fassara: Bilkisu Xin)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Kassim: Duk Wanda Yake Neman Hizbullah Ta Ajiye Makamanta Yana Yi Wa Isra’ila Aiki
Babban magatakardar kungiyar Hizbullah Sheikh Na’im Kassim ya bayyana cewa; Hizbullah tana yin aiki ne ta fuskoki biyu; na farko gwgawarmaya da HKI, sai kuma a fagen Siyasa a cikin gida.
Shugaban kungiyar ta Hizbullah wanda ya gabatar da jawbai a jiya domin girmama babban kwamandan kungiyar Hizbullah Shahid Sayyid Fu’ad Shukr ya ce; An zabi shugaban kasa Joseph Aun ne bayan da aka dauki shekaru ba tare da shugaban kasa ba a kasar. Kuma kungiyar gwagwarmaya ta tabbatar da cewa ginshiki ne a fagen siyasa, wacce ta saukaka yadda aka zabi shugaban kasar da kafa gwamnati.”
Har ila yau Sheikh Naim Kassim ya yi bayani akan yadda gwagwarmaya ta kafu a cikin kasar Lebanon a matsayin mayar da martani ga mamayar HKI, ta kuma cike gibin da sojoji su ka bari, da a karshe a 2000 ta kori HKI daga cikin Lebanon.
Sheik Na’im Kassim ya kuma ce; Gwgawarmaya wani nauyi ne da rataya akan kowa, ba wai zabi ba ne,kuma lokacin da aka yi aiki a tsakanin gwgawarmaya, soja da al’umma an cimma nasarori masu yawan gaske.
Babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah sheik Na’im Kassim ya kuma ce; Batun makaman dake hannun kungiyar Hizbullah wani batu ne da ya shafi cikin gidan kasar Lebanon, don haka ba shi da wata alaka da HKI.”
Akan batun kwance damarar yakin kungiyar ta Hizbullah, Sheikh Na’im Kassim ya ce, duk wanda yake son ganin hakan ta faru, to yana yi wa Isra’ila aiki ne.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Mata July 31, 2025 Tawagar Iran Ta Fice A Taron Majalisun Dokokin Kasashen Duniya A Lokacin Jawabin Wakilin Isra’ila July 31, 2025 Kasar Iran Ta Bayyana Gushewar Hasashen Raunin Karfin Sojinta Kuma Ba Zai Dawo Ba July 31, 2025 Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine July 31, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku July 31, 2025 Qolibaf: Barin HKI Ta Yi Abinda Taga Dama Ne Yana Karfafa Mata Giwa July 30, 2025 Yunwa Ta Kashe Karin Falasdinawa 7 A Gaza July 30, 2025 Malta Zata Amince da Samuwar Falasdinu a Cikin Watan Satumba Mai Zuwa July 30, 2025 Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah July 30, 2025 Siriya Da HKI Zasu Gudanar Da Taro A Baku July 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci