Aminiya:
2025-11-03@10:45:22 GMT

An kama jarkokin manja maƙare da alburusai a Abuja

Published: 25th, March 2025 GMT

Rundunar ‘yan sandan Birnin Tarayya ta ce ta kama damin alburusai 488 da aka ɓoye a jarkar manja a tashar mota.

Mataimakin kwamishinan ‘yan sandan da ke kula da sintiri na musamman a Abuja, DCP Ishaku Sharu, ne ya bayyana hakan lokacin da yake holen wanda ake zargin a ofishin rundunar a ranar Litinin.

Matasa sun daka wawa kan kayan abincin da Seyi Tinubu zai raba a Gombe Gwamnonin PDP sun garzaya Kotun Ƙoli kan dakatar da Gwamnan Ribas

Ya ce rundunar ta samu nasarar kama wanda ake zargin ne bisa tallafin wasu jami’an ƙungiyar masu sufurin motocin haya (NURTW).

Kazalika, ya ce sun kama wanda ake zargin ne ɗan asalin Jihar Katsina, ɗauke da harsashi 488 na bindigogin AK-47 da ya ɓoye a jarkokin manja.

DCP ya ce bayan rutsa shi ne ya bayyana musu cewa wani Yakubu Kacalla ne ɗan garin Funtua da ke Katsinan ya biya shi N100,000 domin karɓo masa kayan daga wajen wani mutum a Jihar Nasarawa.

Yanzu haka dai wanda ake zargin na hannun ‘yan sanda inda suke ci gaba da bincike domin kamo sauran masu hannu a safarar makaman.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Tsaro wanda ake zargin

এছাড়াও পড়ুন:

Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?

Shi ma wasan da ta yi nasara a kan kungiyar Sifaniya a daf da za a tashi ta ci kwallon a gasar Zakarun Turai da na Newcastle United a Premier League. Tun daga nan alamomi suka fara bayyana cewar akwai tarin matsaloli a Liberpool, wadda kowanne wasa kwallo ke shiga ragarta in ban da wanda ta yi nasara a kan Arsenal 1-0 a Premier League cikin Agusta da wanda ta ci Burnley 1-0 a cikin watan Satumba a Premier League.

Sababbnin ‘Yanwasan da Liberpool ta saya a kakar banamages Giorgi Mamardashbili daga Balencia Jeremie Frimpong daga Bayern Leberkusen, Florian Wirtz daga Bayern Leberkusen,

Milos Kerkez daga Bournemouth, Hugo Ekitike daga Eintracht Frankfurt, Aledander Isak daga Newcastle United, Armin Pecsi daga Puskas Akademia. Giobanni Leoni daga Parma Freddie Woodman daga Preston North, Will Wright daga Salford.

Wasu daga cikin matsalolin Liberpool A Yanzu

Matsalar masu buga mata tsakiya Liberpool ta samu sauye-sauye da yawa a fannin masu taka mata wasa daga tsakiya, bayan da wasu daga ciki suka bar kungiyar, ya dace a ce ta hada

fitattun da za ta fuskanci kakar bana.

Liberpool ta dauki Florian Wirtz daga Bayern Leberkusen, amma har yanzu dan wasan bai nuna kansa ba, inda yake ta shan suka daga magoya bayan da suke ganin kwalliya ba za ta biya kudin sabulu ba.

Raunin ‘yanwasa da ke jinya

Raunin da wasu ‘yanwasan Liberpool suka ji sun taka rawar gani da kungiyar Liberpool ke kasa kokari a kakar nan. Daga ciki mai tsaron baya, Giobanni Leoni ya ji rauni a wasansa na farko a kungiyar, wanda ake cewa yana doguwar jinya. Mai tsaron raga Alisson Becker ya ji rauni a lokacin gasar zakarun turai wanda ake cewar zai yi jinya har karshen watan Oktoba, watakila ya wuce hakan.

Bayan Liberpool na yoyo

A kakar bara bayan Liberpool ya yi yoyo, duk da cewar kungiyar ce ta lashe kofin, amma dai an samu matsaloli da yawa a bayan. Kungiyoyi da dama sun amfana da kurakuren Liberpool a bara daga ciki har da Nottingham Forest da Brighton da kuma Brentford.

Wasu lokutan da zarar Liberpool ta kai kora sai kaga wagegen gibi tsakanin masu tsare baya da ‘yan tsakiya. Haka kuma tun kafin fara kakar bana, Liberpool ta buga wasannin atisaye, kuma tun a lokacin gurbin masu tsare baya ya nuna matasalar da kungiyar za ta iya fuskanta da fara

kakar nan.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025? November 1, 2025 Wasanni Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray October 30, 2025 Wasanni Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi October 28, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Yabawa Gwamna Namadi Bisa Ayyukan Hanyoyi A Fadin Jihar
  • Matar aure ta yanka wuyan mijinta, ta fasa masa ido da wuƙa a Neja
  • Yadda matata ta ɓace a Abuja aka tsince ta a Sakkwato
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • Barcelona ta shiga zarwacin Victor Osimhen
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa