Aminiya:
2025-09-18@02:16:29 GMT

Ban bai wa majalisa haƙuri ba — Natasha

Published: 24th, March 2025 GMT

Sanata mai wakilatar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan, ta musanta batun da ake yaɗawa cewa ta bai wa Majalisar Dattawa haƙuri.

A wata sanarwa da ta fitar ranar Litinin, Natasha ta ce tana na kan batunta, kuma ba za ta taɓa bai wa majalisar haƙuri a kan gaskiyarta ba.

Fursunoni 12 sun tsere bayan fasa gidan yari a Kogi Za mu farfaɗo da Madatsar Ruwa ta Biu — Zulum

Idan za a tuna dai majalisar ta dakatar da Natasha tsawon watanni shida tare da dakatar da albashi da alawus-alawus ɗinta ne bisa saɓa wa dokokin majalisar da kwamitin ƙorafi da ladabtarwa ya tabbatar.

Lamarin dai na zuwa ne a daidai lokacin da kuma Sanata Natasha take ci gaba da zargin shugaban majalisar, Godswil Akpabio, da cin zarafinta.

Daga bisani kuma Natasha ta shigar da koken nata a Majalisar Ɗinkin Duniya.

“Zan ci gaba da yaƙi domin ƙwato ‘yancin matan Najeriya har sai ranar da aka fara sauraronmu. Yunƙurin da ake yi domin rufe bakina ba na wasa ba ne, amma ko a jikina.

“Gaskiyar wasan kwaikwayon da ake yi akan idon ‘yan Najeriya za ta bayyana watarana, sannan duk ‘yan rashawar da suka mamaye gwamnatin za su yi bayani dalla-dalla,” in ji Natasha.

“Don haka ina kira gare ku, da ku yi watsi da da duk wani rahoto da kuka ci karo da shi cewa na bai wa majalisa haƙuri, domin ba gaskiya ba ne.

“Ina na kan batuna, kuma zan ci gaba da yaƙi a kan gaskiyata duk rintsi duk wuya.

To sai dai Natasha na wannan maganar ne a daidai lokacin da hukumar zaɓe ta kasa ke bayyana cewa ta samu takardar neman yi wa ‘yar majalisar kiranye daga mazabarta.

Sakatariyar hukumar Rose Oriarana-Anthony ce ta bayyana hakan inda ta ce takardar ta iske ta ne a ranar Litinin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Dattawa Majalisar Dinkin Duniya Zargin Cin Zarafi

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

 

Cikin jadawalin GII na 2025, kasashe masu karanci da matsakaicin kudin shiga 17, sun taka rawar gani fiye da yadda aka yi hasashe, bisa matsayin ci gabansu, yayin da kasashen Afirka dake kudu da hamadar Sahara ke kan gaba, cikin kasashe mafiya samun ci gaban kirkire-kirkire, inda kasashen Afirka ta Kudu, da Senegal da Rwanda ke kan gaba a jerin kasashen shiyyar. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Chadi:  Majalisa ta amince a baiwa shugaban kasa  damar ci gaba da Mulki har karshen rayuwa
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta