Ban bai wa majalisa haƙuri ba — Natasha
Published: 24th, March 2025 GMT
Sanata mai wakilatar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan, ta musanta batun da ake yaɗawa cewa ta bai wa Majalisar Dattawa haƙuri.
A wata sanarwa da ta fitar ranar Litinin, Natasha ta ce tana na kan batunta, kuma ba za ta taɓa bai wa majalisar haƙuri a kan gaskiyarta ba.
Fursunoni 12 sun tsere bayan fasa gidan yari a Kogi Za mu farfaɗo da Madatsar Ruwa ta Biu — ZulumIdan za a tuna dai majalisar ta dakatar da Natasha tsawon watanni shida tare da dakatar da albashi da alawus-alawus ɗinta ne bisa saɓa wa dokokin majalisar da kwamitin ƙorafi da ladabtarwa ya tabbatar.
Lamarin dai na zuwa ne a daidai lokacin da kuma Sanata Natasha take ci gaba da zargin shugaban majalisar, Godswil Akpabio, da cin zarafinta.
Daga bisani kuma Natasha ta shigar da koken nata a Majalisar Ɗinkin Duniya.
“Zan ci gaba da yaƙi domin ƙwato ‘yancin matan Najeriya har sai ranar da aka fara sauraronmu. Yunƙurin da ake yi domin rufe bakina ba na wasa ba ne, amma ko a jikina.
“Gaskiyar wasan kwaikwayon da ake yi akan idon ‘yan Najeriya za ta bayyana watarana, sannan duk ‘yan rashawar da suka mamaye gwamnatin za su yi bayani dalla-dalla,” in ji Natasha.
“Don haka ina kira gare ku, da ku yi watsi da da duk wani rahoto da kuka ci karo da shi cewa na bai wa majalisa haƙuri, domin ba gaskiya ba ne.
“Ina na kan batuna, kuma zan ci gaba da yaƙi a kan gaskiyata duk rintsi duk wuya.
To sai dai Natasha na wannan maganar ne a daidai lokacin da hukumar zaɓe ta kasa ke bayyana cewa ta samu takardar neman yi wa ‘yar majalisar kiranye daga mazabarta.
Sakatariyar hukumar Rose Oriarana-Anthony ce ta bayyana hakan inda ta ce takardar ta iske ta ne a ranar Litinin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Majalisar Dattawa Majalisar Dinkin Duniya Zargin Cin Zarafi
এছাড়াও পড়ুন:
Mutanen Sweida Na Kasar Siriya Suna Fama da Rashin Abinci da Ruwa
A yankin sweida na kudancin kasar Siriya mazauna wurin sun bayyana cewa abinci da ruwa da kuma kayakin bukatu nay au da kullum sun fara karanci sosai a yankin saboda yakin makonni uku da suke fafatawa da sojojin sabuwar gwamnati a Damascus.
Jaridar The National ta Amurka ta bayyana cewa yankin sweida na kudancin kasar Siriya wanda kuma HKI ta dade tana shigowa yankin ta fita a halin nyanzu yana fama da karancin abinci da ruwansha. Sannan da alamun har yanzun sojojin sabuwar gwamnatin kasar Siriya tana ci gaba da hana shigowar abinci da ruwa yankin duk tare da shelanta tsagaita wuta da aka yi.
Labarin ya kara da cewa. an kashe daruruwan mutane a fafatawar da mayakan hTI suka yi da drsawa da suka fi rinjaye a yankin da kuma wasu kananan kabilu a yankin.
Tun lokacinda HKI tare da taimakin kasashen turkiya da sauran kasashen yamma suka kifar da gwamnatin Bashar al-asad, kasar Siriya take fama da karin kashe-kashe na kabilanci da na addini a kasar.