Juventus ta sallami kocinta Thiago Motta
Published: 25th, March 2025 GMT
Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Juventus ta raba gari da mai horas da ’yan wasanta, Thiago Motta, yayin da ko kaka ɗaya bai cika ba a kwantaragin da ya ƙulla da ƙungiyar ta Italiya.
A cewar Jaridar wasanni ta La Gazzetta dello da Gidan Talabijin na Sky Sport, Juventus ta maye gurbin Thiago Motta da tsohon ɗan wasan ƙungiyar, Igor Tudor.
Juventus dai za ta ɗora wa sabon kocin nauyin jajircewa wajen ganin ƙungiyar ta ƙare a cikin sahun huɗun farko na teburin Gasar Serie A ta bana, domin samun damar buga Gasar Zakarun Turai a kaka mai zuwa.
A halin yanzu ƙungiyar da ke fama da rashin kuɗi, ita ce ta biyar a teburin Serie A yayin da ya rage sauran wasanni 9 a ƙarƙare gasar.
Kafofin watsa labarai daga Italiya sun ruwaito cewa nan da kowane lokaci ƙungiyar za ta fitar da sanarwa a hukumance ta raba gari da Thiago Motta mai shekaru 42 da kuma naɗa magajinsa, Igor Tudor.
A watan Yulin bara ne dai Thiago Motta ya karɓi ragamar jagorancin ƙungiyar bayan ya yi ƙoƙari matuƙa a ƙungiyar Bologna a kakar 2023/24.
Sai dai a yanzu duk gwiwowinsa sun yi sanyi sakamakon rashin kataɓus a ƙungiyar da ake yi wa laƙabi da Old Lady.
A ƙarƙashin jagorancin kociyan ɗan ƙasar Brazil, Juventus ta buga wasanni 42, inda ta yi nasara a 18 da canjaras 16 sai kuma rashin nasara a wasanni takwas.
A watan Fabrairun da ya gabata ne ƙungiyar PSV ta koro Juventus daga Gasar Zakarun Turai, sannan Empoli ta fatattako ta daga Kofin Italiya.
Wasanni biyu na bayan nan da Motta ya jagorancin ƙungiyar ta gamu da rashin nasara a hannun Atalanta wadda ta lallasa ta da ci 4-0 — wadda ita ce rashin nasara mafi girma da ta yi a gida tun 1967 — sai kuma kashi da ta sha a hannun Fiorentina da ci 3-0.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Ivory Coast Ouattara zai sake takara wa’adi na huɗu
Shugaban Ivory Coast, Alassane Ouattara wanda ke jagorantar ƙasar tun daga shekarar 2011, na fuskantar suka na neman mayar da shugabancin ƙasar mutu ka raba.
Wannan dai na zuwa ne bayan Ouattara mai shekaru 83 ya tabbatar da aniyar sake takara wa’adi na hudu a zaben da za a yi ranar 25 ga watan Oktoba.
Za mu halasta kafa ƙasar Falasɗinu muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba — Birtaniya Nijar da Rasha sun ƙulla yarjejeniyar makamashin nukiliyaA wani takaitaccen bayani da ya yi, Ouattara ya ce takararsa ta samo asali ne daga buƙatarsa ta kiyaye zaman lafiyar ƙasa a daidai lokacin da ta ke fuskantar kalubalen tsaro da na tattalin arziki.
Ya bayyana cewa, “Ni dan takara ne saboda kundin tsarin mulkin kasarmu ya ba ni damar sake tsayawa takara a wani wa’adi, kuma ina da lafiyar yin hakan,” inji Shugaba Ouattara.
Sanarwar da ya yi a kafafen sada zumunta, na zuwa ne bayan da jam’iyyarsa ta Rally of Houphouëtists for Democracy and Peace (RHDP) ta amince da takararsa a hukumance.
Jam’iyyun adawa sun soki matakin da cewa ya saba wa kundin tsarin mulkin kasar.
Tun dai gabanin sanar da matsayar sake takara, aka soma tafka muhawara kan soke sunayen ’yan takarar shugaban kasa daga bagaren ’yan adawa.
Tsohon shugaban ƙasar Laurent Gbagbo, da tsohon Firaminista Guillaume Soro, da kuma tsohon minista Tidjane Thiam duk an cire sunayensu daga rajistar masu zaɓe, lamarin da ya hana su tsayawa takara.
Bayanai sun ce hankali ya ƙara tashi a yau bayan da hukumomi suka haramta zanga-zangar lumana da aka shirya gudanarwa a ranar 7 ga watan Agusta, ranar bikin samun ’yancin kai na Cote d’Ivoire.
Ƙungiyoyin ’yan adawa ne suka shirya zanga-zangar da nufin neman a gudanar da bincike mai zaman kansa kan jerin sunayen masu kaɗa ƙuri’a tare da mayar da sunayen waɗanda aka hana tsayawa takara.