An Yi Taron Tattaunawar Kasa Da Kasa Kan Damammakin Da Sin Ke Gabatarwa A Rasha
Published: 24th, March 2025 GMT
Babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin, wato CMG ya gabatar da taron tattaunawar kasa da kasa mai taken “Sin a lokacin bazara: More damammakin da take gabatarwa ga duniya” a ran 20 ga watan nan da muke ciki a kasar Rasha. Kuma Shugaban CMG Shen Haixiong ya gabatar da jawabi ta kafar bidiyo.
Jakadan Sin dake kasar Rasha, Zhang Hanhui da wakilan bangaren siyasa da ba da ilmi da yada labarai na kasar Rasha sun halarci taron don tattaunawa kan hadin gwiwar tattalin arzikin kasashen biyu da kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha da musanyar al’adu da kuma hadin kan kafofin yada labarai da sauransu. Wakilai na Rasha sun hada da Andrey Denisov, mataimakin shugaba na farko na kwamiti mai kula da harkokin ketare na tarayyar kasar Rasha, da kuma Alexander Yakovenko, mataimakin babban manajan rukunin yada labarai na“Rossiya Segodnya”,kana da Andrey Margolin, mataimakin shugaban kwalejin nazarin tattalin arziki da harkokin al’umma dake karkashin shugaban Rasha wato (RANEPA), da Yuri Mazei, mataimakin shugaban jami’ar Lomonosov Moscow, kana da Mikhail Chkanikov, babban editan jaridar “Arguments and Facts”. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: kasar Rasha
এছাড়াও পড়ুন:
Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe
Aƙalla Mutane biyar sun kwanta dama wasu huɗu kuma sun jiggata sakamakon tsinkewar igiyar lantarki bayan dawo da wutar lantarkin mai ƙarfi a unguwar Tudun Wadan Pantami, ta jihar Gombe.
Kamar yadda wani mazaunin yankin Adamu Abubakar Kulani, ya shaidawa manema labarai, mummunan lamarin ya faru ne a daren ranar Juma’a yayin da aka kawo wutar lantarkin bayan sun kwashe kwanaki babu ita.
Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Lura Da Yanayin Bala’u Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga MataYa ƙara da cewa sanadiyar wutar ta zo da ƙarfi ne ta haifar da tartsatsi, kana ta tsinka igiyar babban layin lantarkin wanda ta faɗa kan mutanen.
Tuni jama’ar yankin aka garzaya da waɗanda suka jiggata Baban Asibitin Ƙwararru na Jihar Gombe, domin duba lafiyarsu da basu kulawa kana sauran kuma da suka riga mu gidan gaskiya aka yi jana’izarsu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp