A kwanakin nan, birnin Beijing na Sin ya karbi tarin ‘yan siyasa da ‘yan kasuwar kasar Sin dake kawo ziyara kasar, sai dai kuma idan an yi la’akari da yanayin yakin cinikayya tsakanin sassan kasa da kasa dake wakana yanzu haka, a iya cewa ziyarce-ziyarcen sun zo da mamaki.

Yayin da gwamnatin Amurka ke matsa kaimi wajen ingiza yakin cinikayya, ‘yan siyasa da wakilan manyan kamfanonin Amurka na haye wahalhalu inda suke ta kawo ziyara Sin, wanda hakan ke nuni ga matukar goyon baya da salon bude kofar cinikayyar duniya ke samu, da kuma fatan da ake yi na samun cikakken daidaito, da hadin gwiwar raya tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Amurka.

Ko shakka babu, matakin Amurka na kaddamar da yakin cinikayya ta fakewa da “kishin farfado da tattalin arzikin kasa”, ba zai sauya halin da ake ciki na gibin kasuwancin Amurka ba, ko ingiza farfadowar sashen sarrafa hajoji na kasar. Maimakon haka, matakin zai haifar da yanayi ne na koma bayan tattalin arziki, tare da jefa rayukan Amurkawa cikin mummunan yanayi, wanda kuma zai kai ga mayar da Amurka saniyar ware tsakanin kasashen duniya. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Na Da Kwamitoci 30 Da Ke Sa Ido Kan Ma’aikatun Gwamnati

Majalisar Dokokin Jihar Jigawa ta ce akwai kwamitoci guda 30 da aka daurawa nauyin bibiyar yadda ma’aikatu da hukumomin gwamnatin Jihar ke sarrafa kudade domin gudanar da harkokin yau da kullum, gami da ayyukan raya kasa.

 

Shugaban Kwamatin kananan hukumomi na majalisar dokokin jihar, Alhaji Aminu Zakari, ya bayyana hakan lokacin wata ziyarar aiki a karamar hukumar Babura.

Yayi bayanin cewar, an dorawa Kwamatinsa alhakin duba kananan hukumomi domin tabbatar da shugabanci nagari a yankunan karkara.

 

A cewarsa, kwamatin yana duba kundin bayanan sha’anin mulki da na harkokin kudi da suka hada da jadawalin kudaden da karamar hukuma ke samu daga kason arzikin kasa, da littafin hulda da banki,da takardun biyan kudade na voucher da kundin bayanan tarukan kwamitocin karamar hukuma domin tabbatar da ritita kudaden gwamnati.

 

Alhaji Aminu Zakari ya kuma lura cewar, ziyarar tana bada damar ganawa tsakanin ‘yan kwamatin da masu ruwa da tsaki na kananan hukumomi domin tattaunawa da su, da nufin samar da kyakkyawan yanayin aiki tare tsakanin bangarori daban daban.

 

Karamin Kwamatin da wakilin mazabar Guri Alhaji Usman Abdullahi Tura Musari ya jagoranta, ya duba aikin noman shinkafa a fadamar Garu da ta Dangoriba da karamar hukumar Babura ta bullo da shi akan Kudi Naira Milyan 49 da dubu 500, inda aka samar da rijiyoyin ban ruwa dari-dari a kowacce fadama.

 

Alhaji Usman Musari ya kuma yabawa karamar hukumar Babura bisa kyakkyawar aniyarta, ta mara baya ga kokarin gwamnatin Malam Umar Namadi wajen bunkasa tattalin arzikin matasa ta fuskar hadahadar aikin noma.

 

A jawabin sa, shugaban karamar hukumar Babura Malam Hamisu Muhammad Garu, ya bayyana ziyarar a matsayin wani sanannen aiki da Majalisa ke yi duk shekara,  inda ya yi kira ga ma’aikata da ‘yan majalisar zartaswar karamar hukumar da su bada cikakken hadin kai domin samun nasarar ziyarar.

 

Sauran ‘yan kwamatin sun hada da mataimakin shugaban kwamatin kuma wakilin mazabar Kaugama Alhaji Sani Sale Zaburan da wakilin mazabar Kanya Babba Alhaji Ibrahim Hashim Kanya da mataimakan sakatare da Oditoci biyu.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wasu ’yan siyasa na sukar Tinubu saboda ɗan Kudu ne — Onanuga
  • Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki
  • Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da Amurka
  • Shugabannin Hukumomin Watsa Labarai Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya ga Tsohuwar Uwargidan Shugaban Ƙasa Aisha Buhari
  • Jagora: Iran Ta Bayyana Karfinta Da Jajircewarta A Yakin Kwanaki 12 Ga Duniya
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Na Da Kwamitoci 30 Da Ke Sa Ido Kan Ma’aikatun Gwamnati
  • Rasha Ta Mayar Da Martani Ga Shugaban Amurka Kan Gindaya Wa’adin Kawo Karshen Yakin Ukraine
  • Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa
  • An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden