Aminiya:
2025-06-16@23:06:09 GMT

Matasa sun daka wawa kan kayan abincin da Seyi Tinubu zai raba a Gombe

Published: 24th, March 2025 GMT

Wasu fusatattun matasa sun daka wawa kan kayan abincin tallafin azumi da ɗan Shugaba Nijeriya, Seyi Tinubu zai raba a Jihar Gombe.

Aminiya ta ruwaito cewa duk da cewa bai kai ga zuwa jihar ta Gombe ba, amma kayan abinci da zai raba tuni sun isa jihar.

Gwamnonin PDP sun garzaya Kotun Ƙoli kan dakatar da Gwamnan Ribas Ban bai wa majalisa haƙuri ba — Natasha

Wani bidiyo da ya karaɗe shafukan sada zumunta, ya nuna matasan na wawason katan-katan na kayan abinci daga kan wata mota da ke tsaye a bakin titi.

An hangi matasan na jefa wa waɗanda ke ƙasa kayan abincin — inda suke karɓa su kama gabansu.

Kayan abincin sun haɗa da buhunan shinkafa da sikari da mai da taliya da kuma gishiri.

Yayin da tuni an raba ɗaya daga cikin motocin ɗauke da kayan abincin, matasan sun tare guda inda suka yi wawushe komai da ke cikinta.

A bayan nan dai ɗan gidan shugaban ƙasar na shawagi a wasu jihohin arewacin Nijeriya, inda yake haɗuwa da mazauna jihohin da kuma shugabannin siyasa wajen buɗa-baki.

A yayin waɗannan ziyarce-ziyarce ne kuma ɗan shugaban ƙasar yake ƙaddamar da rabon tallafin abinci ga mabuƙata da albarkacin watan azumi.

Sai dai wannan lamari na ci gaba da janyo cece-kuce a faɗin ƙasar, a yayin da wasu ke yabawa wasu ko kushe suke yi.

Tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido, ya yi Allah wadai da rabon abincin da ɗan shugaban ƙasar ya yi a yankin Arewa, yana bayyana hakan a matsayin wani nau’i na rashin mutunta al’adun Arewa.

A cikin wani bidiyo da karaɗe shafukan sada zumunta, Lamido ya bayyana hakan a yayin wani taron buɗa-baki na mambobin jam’iyyar PDP da ya gudana a garin Bamaina da ke Ƙaramar Hukumar Birnin Kudu ta Jihar Jigawa.

A makon jiya ne ɗan gwamnan Bauchi, Shamsuddeen Bala Mohammed, ya yi kira ga Seyi Tinubu da ya yi amfani da ziyararsa don tallafa wa matasan jihar.

Shamsuddeen Bala Mohammed ya ce bai kamata a mayar da matasan Bauchi kamar mabarata ba, sai dai a ba su damar dogaro da kansu ta hanyar ayyukan yi da horo na musamman.

Shamsuddeen ya bayyana cewa matasan Bauchi sun fi buƙatar ayyukan yi da jari, ba kayan abinci kawai ba.

Ya buƙaci a ba su tallafi kamar Keke NAPEP, kuɗin kafa kasuwanci, da kuma horo a fannin sadarwar zamani da cinikayyar kirifto domin inganta rayuwarsu.

Ɗan gwamnan na Bauchi ya ce yana da kyau a koya wa matasa yadda za su dogara da kansu fiye da ba su abinci da zai kare a rana ɗaya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: jihar Gombe Kayan abinci kayan abincin kayan abinci

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe

Dakarun Operation Haɗin Kai sun kama mut biyar da ake zargin suna taimaka wa ’yan ta’adda da kayan aiki.

Daga cikinsu har da wani ɗan ƙasar China da ya ce shi mai harkar ma’adinai ne.

Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya

An kama su ne a lokacin kai wani samame da aka gudanar daga 5 zuwa 7 ga watan Yuni a ƙananan hukumomin Kukawa da Ngala na Jihar Borno, da kuma Geidam a Jihar Yobe.

A lokacin wannan aiki, dakarun sun ƙwato wasu kayayyaki da suka haɗa da mota, babur, wayoyin salula, fasfo na ƙasar China, da kuma kuɗi Naira 10,000.

Shugaban sashen yaɗa labaran tsaro, Manjo Janar Edward Markus Kangye, ya bayyana hakan a wata ganawa da manema labarai a Abuja.

Ya ce sojojin sun kuma kai farmaki wasu yankuna bisa bayanan sirri da suka samu, ciki har da Gwoza da Abadam a Borno da kuma Nangere a Yobe, daga 6 zuwa 9 ga watan Yuni.

Ya ƙara da cewa daga 6 zuwa 11 ga watan Yuni, wasu maza da mata da yara da dama sun miƙa wuya ga dakarun Najeriya.

Kangye ya bayyana cewa rundunar ta kuma kai wasu hare-hare tare da haɗin gwiwar jami’an tsaro a Ngala, Marte, Gwoza a Jjihar Borno da Bade da Gujba a Jihar Yobe daga 6 zuwa 10 ga watan Yuni.

A wannan lokaci, sun lalata sansanonin ’yan ta’adda, sun ƙwato makamai da alburusai.

Manjo Janar Kangye ya ce sojojin Najeriya za su ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin ’yan ƙasa tare da tabbatar da doka da oda.

“Mun ƙudiri aniyar kare martabar Najeriya da tabbatar da zaman lafiya a kowane yanki na ƙasar nan. Wannan aiki namu na ci gaba da yin tasiri,” in ji shi.

Ya buƙaci haɗin kan jama’a wajen taimaka wa sojoji su ci gaba da yaƙi da ’yan ta’adda.

Ya ce idan jama’a da hukumomi suka haɗa kai, Najeriya za ta samu zama lafiya da wadata.

“Zamu ci gaba da sanar da al’umma duk wani ci gaba da muka samu wajen yaƙar ta’addanci,” in ji Kangye.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya bayar da umarnin binciken hare-haren Benuwe
  • Tinubu ya bayar umarnin binciken hare-haren Benuwe
  • Sabon harin Iran ya hallaka mana mutum 8 – Isra’ila
  • An tallafa wa mata 250 da abinci da kayan sana’a a Kaduna
  • Yadda wani ɗan sanda ya rasu a hanyar zuwa ɗaurin aurensa
  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe
  • DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci