Aminiya:
2025-11-03@01:54:17 GMT

Matasa sun daka wawa kan kayan abincin da Seyi Tinubu zai raba a Gombe

Published: 24th, March 2025 GMT

Wasu fusatattun matasa sun daka wawa kan kayan abincin tallafin azumi da ɗan Shugaba Nijeriya, Seyi Tinubu zai raba a Jihar Gombe.

Aminiya ta ruwaito cewa duk da cewa bai kai ga zuwa jihar ta Gombe ba, amma kayan abinci da zai raba tuni sun isa jihar.

Gwamnonin PDP sun garzaya Kotun Ƙoli kan dakatar da Gwamnan Ribas Ban bai wa majalisa haƙuri ba — Natasha

Wani bidiyo da ya karaɗe shafukan sada zumunta, ya nuna matasan na wawason katan-katan na kayan abinci daga kan wata mota da ke tsaye a bakin titi.

An hangi matasan na jefa wa waɗanda ke ƙasa kayan abincin — inda suke karɓa su kama gabansu.

Kayan abincin sun haɗa da buhunan shinkafa da sikari da mai da taliya da kuma gishiri.

Yayin da tuni an raba ɗaya daga cikin motocin ɗauke da kayan abincin, matasan sun tare guda inda suka yi wawushe komai da ke cikinta.

A bayan nan dai ɗan gidan shugaban ƙasar na shawagi a wasu jihohin arewacin Nijeriya, inda yake haɗuwa da mazauna jihohin da kuma shugabannin siyasa wajen buɗa-baki.

A yayin waɗannan ziyarce-ziyarce ne kuma ɗan shugaban ƙasar yake ƙaddamar da rabon tallafin abinci ga mabuƙata da albarkacin watan azumi.

Sai dai wannan lamari na ci gaba da janyo cece-kuce a faɗin ƙasar, a yayin da wasu ke yabawa wasu ko kushe suke yi.

Tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido, ya yi Allah wadai da rabon abincin da ɗan shugaban ƙasar ya yi a yankin Arewa, yana bayyana hakan a matsayin wani nau’i na rashin mutunta al’adun Arewa.

A cikin wani bidiyo da karaɗe shafukan sada zumunta, Lamido ya bayyana hakan a yayin wani taron buɗa-baki na mambobin jam’iyyar PDP da ya gudana a garin Bamaina da ke Ƙaramar Hukumar Birnin Kudu ta Jihar Jigawa.

A makon jiya ne ɗan gwamnan Bauchi, Shamsuddeen Bala Mohammed, ya yi kira ga Seyi Tinubu da ya yi amfani da ziyararsa don tallafa wa matasan jihar.

Shamsuddeen Bala Mohammed ya ce bai kamata a mayar da matasan Bauchi kamar mabarata ba, sai dai a ba su damar dogaro da kansu ta hanyar ayyukan yi da horo na musamman.

Shamsuddeen ya bayyana cewa matasan Bauchi sun fi buƙatar ayyukan yi da jari, ba kayan abinci kawai ba.

Ya buƙaci a ba su tallafi kamar Keke NAPEP, kuɗin kafa kasuwanci, da kuma horo a fannin sadarwar zamani da cinikayyar kirifto domin inganta rayuwarsu.

Ɗan gwamnan na Bauchi ya ce yana da kyau a koya wa matasa yadda za su dogara da kansu fiye da ba su abinci da zai kare a rana ɗaya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: jihar Gombe Kayan abinci kayan abincin kayan abinci

এছাড়াও পড়ুন:

PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike

Rikici a babbar jam’iyyar adawa ta PDP, na ƙara ƙamari, bayan da jam’iyyar ta dakatar da sakatarenta na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, da wasu da ake ganin ’yan tsagin Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike ne.

Mai magana da yawun jam’iyyar na ƙasa, Debo Ologunagba ne, ya sanar da dakatarwar bayan wani taro da Kwamitin Ayyuka na Ƙasa (NWC), ya gudanar a hedikwatar jam’iyyar da ke Abuja.

Zargin Kisan Kiristoci: Maganar Trump a kan Najeriya tsagwaron ƙarya ce — Shehu Sani Zaɓen Tanzania: Shugaba Samia ta yi tazarce da kashi 97 an ƙuri’u

Sauran da aka dakatar sun haɗa da Mai Bai wa jam’iyyar Shawara kan Harkokin Shari’a, Kamaldeen Ajibade (SAN); Sakataren Tsara Harkokin Jam’iyya, Umar Bature; da Mataimakin Mai Bai wa jam’iyyar Shawara kan Harkokin Shari’a.

Rahotanni sun bayyana cewa waɗanda aka dakatar ba sa halartar tarukan jam’iyyar.

An dakatar da su na tsawon wata ɗaya, sannan aka miƙa lamarinsu ga Kwamitin Ladabtarwa na jam’iyyar PDP domin gudanar da bincike.

Waɗanda aka dakatar ’yan tsagin Wike ne, kuma sun raba ƙafa a rikicin da jam’iyyar ke fuskanta tun bayan zaɓen 2023.

Idan ba a manta ba, a ranar Juma’a ne, wata Babbar Kotu a Babban Birnin Tarayya, ta dakatar da PDP daga shirin gudanar da babban taronta da aka tsara yi a Ibadan, Jihar Oyo, a ranar 15 da 16 ga watan Nuwamba, 2025.

Sai dai jam’iyyar ta ce za ta ɗaukaka ƙara kan hukuncin, kuma hakan ba zai hana ta ci gaba da shirye-shiryen gudanar da taron ba.

Wasu daga cikin ’ya’yan jam’iyyar sun ce rashin jituwa a PDO shi ne babban dalilin da ya sa aka kai ƙarar taron’ kotu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Karamar Hukumar Bubura Ta Kai Tallafin Kayayyakin Abinci Cibiyar Gyaran Hali
  • Tinubu ya yanke hulɗa da Amurka kawai — Sheikh Gumi
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon barazana — Kwankwaso
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon ba barazana ba — Kwankwaso
  • Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza
  • Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya 
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike
  • Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
  • Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar