Gidauniyar Bafarawa Ta Rabawa Kananan ‘Yan Kasuwa Naira Milliyan 13 a Sokoto
Published: 13th, March 2025 GMT
Gidauniyar Attahiru Bafarawa ta fara rabon tallafin kudi naira miliyan goma sha uku da dubu dari takwas ga iyaye mata marayu dari biyu da saba’in da bakwai da masu bukata ta musamman a jihar Sokoto domin tallafawa kananan sana’o’i.
Da yake jawabi a wajen kaddamar da shirin, Shugaban shirin, Malam Lawal Maidoki ya bayyana cewa, matakin ya yi daidai da kudurin wanda ya kafa na rage radadin tattalin arziki a tsakanin marasa galihu.
Ya bayyana cewa an zabo mutane 12 da suka ci gajiyar tallafin daga kowace karamar hukumar jihar 23 da suka hada da zawarawa 10 ko marayu mata da kuma nakasassu biyu a kowace karamar hukumar.
Ya ce kowane wanda ya ci gajiyar shirin zai karbi naira dubu hamsin tare da tallafin sufurin daga naira 3,000 zuwa naira 5,000, ya danganta da nisan su da wuraren rabon kayayyakin.
Maidoki ya jaddada cewa shirin na da nufin wadata wadanda suka samu tallafin jarin da ake bukata domin biyan bukatunsu na yau da kullum da kuma samar da kudaden shiga, da karfafa tattalin arzikin kasa.
Da yake jawabi a wajen taron, Sarkin Malaman Sokoto, Malam Yahaya Boyi, ya yabawa tsohon Gwamna, Alhaji Attahiru Bafarawa bisa wannan karamci da ya nuna.
Ya mika godiyar wadanda suka amfana, sannan ya bukace su da su yi addu’a ga masu hannu da shuni, Jihar Sakkwato, da Nijeriya, musamman a wannan wata na Ramadan mai albarka.
Boyi ya kuma ja hankalin wadanda suka karba da su yi amfani da kudaden da suka dace ta hanyar yin sana’o’i masu inganci maimakon yin bara.
Daya daga cikin wadanda suka ci gajiyar shirin, Shehu Gwiwa, ya bayyana godiya a madadin sauran jama’a, inda ya gode wa wannan gidauniya bisa tallafin da ta bayar, ya kuma yi addu’ar Allah ya sakawa duk masu hannu a wannan shirin.
Nasir Malali
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Bafarawa Rabo Sakkwato wadanda suka
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
Hukumomin ’yan sandan Najeriya tare da haɗin gwiwar wasu hukumomin tsaro sun samu gagarumar nasara a ƙoƙarin da suke na daƙile munanan laifuka a ƙasar.
Na baya-bayan nan dai shi ne ceto mutanen da aka sace, da kashe wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne da kuma ƙwato manyan bindigogi da alburusai a jihohin Delta da Katsina.
Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — Dalung An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a AustraliaA wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan, Olumuyiwa Adejobi ya fitar, ya ce a jihar Katsina an samu gagarumar nasara a ranar 8 ga watan Yunin 2025, inda haɗin gwiwar JTF da suka haɗa da jami’an ’yan sanda da sauran jami’an tsaro suka daƙile wani yunƙurin yin garkuwa da mutane a hanyar ƙauyen Danmusa zuwa Mara Dangeza a ƙaramar hukumar Danmusa.
Adejobi ya ce hakan na iya yiwuwa ne ta hanyar shigar da wasu gungun ’yan bindiga da suka yi yunƙurin guduwa da waɗanda aka yi garkuwa da su a wani artabu da ya kai ga ceto mutum 11.
Nasarar da aka samu yankin Kudu maso KuduA halin da ake ciki kuma, a yankin Kudu maso Kudu, Jihar Delta, hukumar ’yan sanda ta kama wani Abubakar Hassan, wanda babban wanda ake zargi da aikata laifin satar mutane ne a tsakanin jihohin Delta da Ribas da Imo, da Enugu.
Jami’an da ke da alaƙa da samun nasarar sun yi hakan ne yayin da suke aiki da sahihan bayanai.
A yayin da ake yi masa tambayoyi, Hassan ya bayyana cewa shi ne ya jagoranci gudanar da hari a yankin Ughelli-Ozoro na jihar mai arzikin man fetur.
Ya kuma jagoranci jami’an ’yan sanda zuwa maɓoyarsa a wani daji da ke Ozoro. A can jami’an sun ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda biyu da tarin alburusai huɗu da harsashi guda talatin da biyu.