Gidauniyar Bafarawa Ta Rabawa Kananan ‘Yan Kasuwa Naira Milliyan 13 a Sokoto
Published: 13th, March 2025 GMT
Gidauniyar Attahiru Bafarawa ta fara rabon tallafin kudi naira miliyan goma sha uku da dubu dari takwas ga iyaye mata marayu dari biyu da saba’in da bakwai da masu bukata ta musamman a jihar Sokoto domin tallafawa kananan sana’o’i.
Da yake jawabi a wajen kaddamar da shirin, Shugaban shirin, Malam Lawal Maidoki ya bayyana cewa, matakin ya yi daidai da kudurin wanda ya kafa na rage radadin tattalin arziki a tsakanin marasa galihu.
Ya bayyana cewa an zabo mutane 12 da suka ci gajiyar tallafin daga kowace karamar hukumar jihar 23 da suka hada da zawarawa 10 ko marayu mata da kuma nakasassu biyu a kowace karamar hukumar.
Ya ce kowane wanda ya ci gajiyar shirin zai karbi naira dubu hamsin tare da tallafin sufurin daga naira 3,000 zuwa naira 5,000, ya danganta da nisan su da wuraren rabon kayayyakin.
Maidoki ya jaddada cewa shirin na da nufin wadata wadanda suka samu tallafin jarin da ake bukata domin biyan bukatunsu na yau da kullum da kuma samar da kudaden shiga, da karfafa tattalin arzikin kasa.
Da yake jawabi a wajen taron, Sarkin Malaman Sokoto, Malam Yahaya Boyi, ya yabawa tsohon Gwamna, Alhaji Attahiru Bafarawa bisa wannan karamci da ya nuna.
Ya mika godiyar wadanda suka amfana, sannan ya bukace su da su yi addu’a ga masu hannu da shuni, Jihar Sakkwato, da Nijeriya, musamman a wannan wata na Ramadan mai albarka.
Boyi ya kuma ja hankalin wadanda suka karba da su yi amfani da kudaden da suka dace ta hanyar yin sana’o’i masu inganci maimakon yin bara.
Daya daga cikin wadanda suka ci gajiyar shirin, Shehu Gwiwa, ya bayyana godiya a madadin sauran jama’a, inda ya gode wa wannan gidauniya bisa tallafin da ta bayar, ya kuma yi addu’ar Allah ya sakawa duk masu hannu a wannan shirin.
Nasir Malali
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Bafarawa Rabo Sakkwato wadanda suka
এছাড়াও পড়ুন:
An Bayyana Ranar Karshe Ta Biyan Kudin Aikin Hajji Mai Zuwa
Hukumar Kula da jin dadin mahajjan Jihar Taraba ta bayyana 1 ga Disamba, 2025, a matsayin ranar ƙarshe ga masu niyyar yin hajji don kammala biyan kuɗin tafiyar hajji ta shekarar 2026.
A cewar wata sanarwa da Sashen Bayani na Hukumar ya fitar ta bakin Mataimakin Daraktan Hamza Baba Muri, an ƙayyade sabon kuɗin hajjin 2026 a Naira miliyan 7,630,000, kamar yadda Hukumar Hajj ta Kasa (NAHCON) ta amince.
Hukumar ta yi kira ga duk masu shirin yin hajji ta wannan tsari su tabbata sun biya kuɗin gaba ɗaya kafin ƙarshen wa’adin domin samun tabbacin shiga cikin masu sauke farali shekara mai zuwa.
Mai magana da yawun Hukumar ya jaddada cewa dukkan biyan kuɗi dole ne a yi su ta hannun Jami’an Cibiyoyin da aka keɓe, yana mai gargadin cewa ba za a karɓi korafi ba bayan wa’adin ƙarshe.
Ya bayyana cewa biyan kuɗi a kan lokaci zai bai wa Hukumar damar tattara jerin sunayen fasinjojin ƙarshe da kuma tura kuɗaɗen zuwa NAHCON bisa jadawalin ƙasa.
Haka kuma, mai magana da yawun Hukumar ya ce ana ci gaba da tattaunawa da masu samar da ayyuka a Saudi Arabia domin tabbatar da abinci mai inganci da wuraren kwana ga fasinjoji a Makkah yayin hajjin 2026.
Hukumar ta sake jaddada kudirinta na samar da mafi kyawun ayyuka ga fasinjojin Taraba, bisa manufa da burin Gwamnatin K-move.
END/JAMILA ABBA