An Bada Umarnin Sake Tsugunar Da Wadanda Harin ‘Yan Bindiga Ya Rutsa Da Su A Kebbi
Published: 13th, March 2025 GMT
Gwamna Nasir Idris na jihar Kebbi, ya ba da umarnin cewa, wadanda harin da ‘yan bindiga suka kai a sansanin ‘yan gudun hijira da ke karamar hukumar Arewa ta jihar, su koma gidajensu nan da makonni biyu masu zuwa bayan an dauki matakai a yankunan da lamarin ya shafa.
Gwamnan, ya ba da umarnin ne a lokacin da ya kai ziyarar jaje sansanin ‘yan gudun hijira da ke Kangiwa da Lakurawa suka kai musu hari tare da raba su da muhallansu a kauyukan Birnin Debe, Dan Marke da Tambo.
Gwamnan ya ce, ya kai ziyarar ne domin jajanta wa wadanda abin ya shafa tare da ba shi damar samun rahoton halin da ake ciki a kan wannan mummunan lamari don jagorantar gwamnatin jihar ta dauki matakin da ake bukata tare da tantance halin da ake ciki da kuma tabbatar da matakan da suka dace da za a dauka cikin gaggawa domin kai daukin gaggawa ga wadanda abin ya shafa.
A yayin da yake koka da cewa, ana kai hare-haren ne daga jihar Sokoto da ke makwabtaka da Jamhuriyar Nijar, Gwamnan ya nuna rashin jin dadinsa kan asarar rayuka da dukiyoyi da aka yi, ya kuma yaba wa jami’an tsaro da suka yi iya kokarinsu wajen ganin an shawo kan lamarin, ya kuma bukaci jama’a da su rika kai rahoton duk wani motsi da suka samu ga hukuma domin daukar matakin da ya dace.
Tun da farko Shugaban Karamar Hukumar Arewa Alhaji Sani Aliyu ya godewa Gwamnan bisa daukar matakin gaggawa don ganin an shawo kan wannan mummunan lamari.
Shugaban ya kuma bayyana cewa an bayar da agajin ga wadanda abin ya shafa, inda ya ce iyalan kowannen wadanda suka rasa rayukansu sun samu Naira 500,000 yayin da kowanne daga cikin wadanda suka jikkata kuma ya samu N500,000.
A ranar Lahadin da ta gabata ne ‘yan bindigar Lakurawa suka kai hari kauyuka 7 a karamar hukumar Arewa ta jihar Kebbi inda suka kashe sama da mutane 10 tare da kona gidaje da dama wanda hakan ya kasance harin ramuwar gayya biyo bayan kashe wani shugabansu mai suna Maigemu da jami’an tsaro suka yi.
Abdullahi Tukur
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun kashe mutum 13 a ƙauyukan Neja
Aƙalla mutum 13 ne suka rasu, ciki har da ɗan sanda da ’yan sa-kai guda uku, a wani hari da ’yan bindiga suka kai garin Mongoro da ke Ƙaramar Hukumar Mariga, a Jihar Neja.
Harin ya faru ne da misalin ƙarfe 5 na yammacin ranar Laraba.
Ana zargin takalar faɗa tsakanin fadar Aminu Ado da Sanusi II ’Yan ƙabilar Ibo ne suka fi aikata laifi a Jihar Anambra ba Fulani ba — Gwamna SoludoMazauna garin Wamba, sun ce har yanzu suna cikin fargaba saboda ‘yan bindigar ba su bar yankin ba.
A ranar 24 ga watan Yuni, maharan sun kai hari wani sansanin sojoji da ke Kwanan-Dutse, inda suka kashe sojoji 17, tare da jikkata wasu 10.
A cewar wasu mazauna garuruwan, harin na baya-bayan nan ya faru ne a ranar Talata, inda ’yan bindigar suka zo da yawa kuma ɗauke da muggan makamai inda suka yi wa jami’an tsaro da ’yan sa-kai taron dangi.
Sun raunata mutane da dama.
Wani mazaunin yankin wanda ya nemi a ɓoye sunansa, ya ce jami’an tsaron sun yi ƙoƙari, amma alburusansu sun ƙare a yayin artabun, wanda hakan ya sa dole suka ja da baya.
Ya ce ana buƙatar gaggauta tallafa wa ’yan sa-kai a Mongoro saboda yankin na fama da hare-hare.
Wani mazaunin kuma ya ce an kashe mutum 13, ciki har da ’yan sa-kai, sannan ’yan bindigar sun lalata turakun sadarwa, wanda hakan ya haddasa matsalar sadarwa a yankin.
Shugaban Ƙaramar Hukumar Mariga, Abbas Adamu Kasuwan-Garba, ya tabbatar da harin, amma ya ce ba a tabbatar da adadin waɗanda suka rasu ba tukuna.
Ya ƙara da cewa lamarin tsaro a yankin na ƙara taɓarɓarewa saboda yawan hare-haren da ake kai wa.
Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar harin, amma ya ce har yanzu babu cikakken bayani.
Saboda tsoron kai hare-haren, manoma da dama a Mariga da Rijau sun daina zuwa gonaki, wasu kuma sun koma birane domin tsira da rayukansu.
Wani mazaunin yankin Rijau, mai suna Ibrahim Ayuba, ya ce mutane da yawa sun tsere daga ƙauyuka zuwa Rijau saboda tsoron kashe-kashe da sace-sacen da ke ƙaruwa a kullum.
A wani yunƙuri na shawo kan matsalar tsaro, Etsu Nupe kuma Shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Jihar Neja, Alhaji Yahaya Abubakar, ya buƙaci haɗin gwiwa da sabbin dabaru domin magance matsalar.
Ya bayyana haka ne yayin da Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, Adamu Abdullahi Elleman, ya kai masa ziyara a fadarsa.
Kwamishinan, ya ce manufar ziyarar ita ce ƙarfafa haɗin kai tsakanin sarakuna, al’umma da jami’an tsaro wajen yaƙi da ’yan bindiga da sauran matsalolin tsaro.
Masani ya buƙaci kafa rundunar tsaron dajiWani masani kan harkar tsaro, Auwal Bala Durumin Iya, ya buƙaci gwamnati ta bai wa ’yan sa-kai da jami’an tsaro makaman da suka fi ‘yan bindiga nagarta.
Ya kuma bayar da shawarar a kafa sabuwar rundunar tsaro domin kula da dazuka, wanda yawancin a can ake aikata laifuka.
Ya ce dole ne a horas da dakarun rundunar sosai, a ba su makamai irin su AK-47, sannan a cire siyasa wajen kula da harkar tsaro.
Ya ce idan aka daina siyasantar da harkar tsaro, aka mayar da hankali kan ƙwarewa, za a iya cimma nasara.
Ya kuma buƙaci gwamnati ta naɗa shugabanni nagari a hukumomin tsaro, tare da tallafa wa ’yan sa-kai da kuɗi da kayan aiki, inda ya yaba wa ƙoƙarinsu duk da cewa ba sa karɓar albashi.