An Bada Umarnin Sake Tsugunar Da Wadanda Harin ‘Yan Bindiga Ya Rutsa Da Su A Kebbi
Published: 13th, March 2025 GMT
Gwamna Nasir Idris na jihar Kebbi, ya ba da umarnin cewa, wadanda harin da ‘yan bindiga suka kai a sansanin ‘yan gudun hijira da ke karamar hukumar Arewa ta jihar, su koma gidajensu nan da makonni biyu masu zuwa bayan an dauki matakai a yankunan da lamarin ya shafa.
Gwamnan, ya ba da umarnin ne a lokacin da ya kai ziyarar jaje sansanin ‘yan gudun hijira da ke Kangiwa da Lakurawa suka kai musu hari tare da raba su da muhallansu a kauyukan Birnin Debe, Dan Marke da Tambo.
Gwamnan ya ce, ya kai ziyarar ne domin jajanta wa wadanda abin ya shafa tare da ba shi damar samun rahoton halin da ake ciki a kan wannan mummunan lamari don jagorantar gwamnatin jihar ta dauki matakin da ake bukata tare da tantance halin da ake ciki da kuma tabbatar da matakan da suka dace da za a dauka cikin gaggawa domin kai daukin gaggawa ga wadanda abin ya shafa.
A yayin da yake koka da cewa, ana kai hare-haren ne daga jihar Sokoto da ke makwabtaka da Jamhuriyar Nijar, Gwamnan ya nuna rashin jin dadinsa kan asarar rayuka da dukiyoyi da aka yi, ya kuma yaba wa jami’an tsaro da suka yi iya kokarinsu wajen ganin an shawo kan lamarin, ya kuma bukaci jama’a da su rika kai rahoton duk wani motsi da suka samu ga hukuma domin daukar matakin da ya dace.
Tun da farko Shugaban Karamar Hukumar Arewa Alhaji Sani Aliyu ya godewa Gwamnan bisa daukar matakin gaggawa don ganin an shawo kan wannan mummunan lamari.
Shugaban ya kuma bayyana cewa an bayar da agajin ga wadanda abin ya shafa, inda ya ce iyalan kowannen wadanda suka rasa rayukansu sun samu Naira 500,000 yayin da kowanne daga cikin wadanda suka jikkata kuma ya samu N500,000.
A ranar Lahadin da ta gabata ne ‘yan bindigar Lakurawa suka kai hari kauyuka 7 a karamar hukumar Arewa ta jihar Kebbi inda suka kashe sama da mutane 10 tare da kona gidaje da dama wanda hakan ya kasance harin ramuwar gayya biyo bayan kashe wani shugabansu mai suna Maigemu da jami’an tsaro suka yi.
Abdullahi Tukur
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
Taron kaddamar da rabar da taraktocin noman, ya gudana ne a Shalkwatar Ma’aikatar Kula da Aikin noma da kuma yin Noman Rani da ke garin Kalaba.
Kazalika, taron ya samu halartar ‘yan Majalisa da Sarakunan Gargajiya da kungiyoyin manoma mata da masu ruwa da tsaki a fannin aikin noma da ke jihar da abokan hadaka.
Daukacinsu, sun jinjina wa wannan kokari na gwamna Bassey, kan wannan hangen nesa da gwamnatinsa ta yi, na kaddamar da taraktocin noman, musamman domin ciyar da fannin aikin noman jihar gaba, duba da cewa; fannin ne kinshikin tattalin arzikin jihar.
Har ila yau, gwamna Bassey, ya nanata kudurin gwamnatinsa wajen ci gaba da bai wa fannin aikin noma muhimmanci a matsayin fannin da ke kara habaka tattalin arzikin jihar.
“A lokacin da na karbi jan ragamar shugabancin jihar, mun samar da dabaru da kuma daukar matakai daban-daban, domin kara habaka fannin,“ in ji gwamna Bassey.
“Biyo bayan wata ganawa da muka yi da manoman da ke daukacin kananan hukumominmu, mun gano cewa; kalubalen da suke fuskanta sama da kashi 70 cikin dari, na shiye-shiyen share gonakansu ne, domin fara noma su; saboda kudaden da suke kashewa masu yawa, wajen gyaran gonakin nasu, muna da yakinin wannan shirin zai magance wadannan matsaloi,” a cewar gwamnan.
Kazalika, gwamnan ya bayyana cewa; wannan rabar da taraktocin noma, wadanda ba sa shan man sosai, an tsara su ne kan yadda manoma za su yi gyaran gonakinsu cikin sauki tare kuma da rage musu kashe kudade masu yawa da kuma kara habaka fannin na aikin noma.
“Kashi 108 na kashin farko na shirin, an raba wa manoman jihar jimillar taraktocin noma 324, wadanda kuma aka rabar da su a daukacin fadin jihar,“ a cewar gwamnan.
Gwamna Bassey ya ci gaba da cewa, za a ci gaba da kula da taraktocin ne a karkashin tsarin kungiyoyin manoma na jihar.
“Hakan zai bai wa wadanda suka amfana da taraktocin damar daukar nauyin ci gaba da kula da su, wanda kuma sauran manoman da ke karkara a jihar, su ma za su samu damar samun taraktocin,” in ji shi.
“Ta wannan hanyar, za mu samu damar cin gajiyar da ke fannin noma na jihar, wanda hakan zai kuma bai wa manoman jihar kara dagewa, domin yin noma da samun kudaden shiga da kuma kara samar da wadataccen abinci a jihar,” a cewar tasa.
Kazalika, gwamnan ya kuma zayyano wasu ayyukan noma da gwamnatinsa ta kaddamar da su da suka hada da na samar da Irin noman Rogo, aikin noman Masara da na Waken Soya da sauransu.
Ya bayyana cewa, gwamnatin na kuma ci gaba da habaka samar da Irin Farin Wake da rabar da kayan aikin noma ga kananan manoma tare da kuma shirye-shiyen noman Koko (Cocoa) da Ganyen Shayi, wanda za gudanar ta hanyar yin hadaka da gwamnatin da kuma ‘yan kasuwa.
“Kaddamar da rabar da wadannan taraktocin noman, na daya daga cikin kason farko na kudurin gwamnatinmu na bunkasa fannin aikin noma na jihar, musamman ta hanyar yin amfani da kayan aikin noma na zamani,” in ji gwamnan.
Shi ma, shugaban kamfanin da ya yi kwangilar kawo taraktocin, Femi Odeshirin, ya yaba wa shirin, wanda ya ce; hakan zai kara bunkasa fannin aikin noma na jihar.
“Ba wai kawai rabar da wadannan taraktocin noma ga manoman jihar ba ne da gwamnan ya yi ba, hakan zai kuma kara inganta rayuwar manoman da suka amfana,” in ji Odeleye.
Ya bayyana cewa, kamfanin na kuma kan shirin kafa masana’antar da ake hada taraktocin noma a garin Kalaba da ke jihar, inda masana’antar za ta samar da ayyukan yi sama da 2,000.
Shi kuwa, shugaban kungiyar manoma ta kasa (AFAN) reshen jihar, Ojikpong Nyiam Bisong, danganta salon shugabancin gwamna Bassey ya yi da na marigayi tsohon Firimiyan Kudancin Nijeriya, Dakta Michael Okpara.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA