Gwamna Nasir Idris na jihar Kebbi, ya ba da umarnin cewa, wadanda harin da ‘yan bindiga suka kai a sansanin ‘yan gudun hijira da ke karamar hukumar Arewa ta jihar, su koma gidajensu nan da makonni biyu masu zuwa bayan an dauki matakai a yankunan da lamarin ya shafa.

 

Gwamnan, ya ba da umarnin ne a lokacin da ya kai ziyarar jaje sansanin ‘yan gudun hijira da ke Kangiwa da Lakurawa suka kai musu hari tare da raba su da muhallansu a kauyukan Birnin Debe, Dan Marke da Tambo.

 

Gwamnan ya ce, ya kai ziyarar ne domin jajanta wa wadanda abin ya shafa tare da ba shi damar samun rahoton halin da ake ciki a kan wannan mummunan lamari don jagorantar gwamnatin jihar ta dauki matakin da ake bukata tare da tantance halin da ake ciki da kuma tabbatar da matakan da suka dace da za a dauka cikin gaggawa domin kai daukin gaggawa ga wadanda abin ya shafa.

 

A yayin da yake koka da cewa, ana kai hare-haren ne daga jihar Sokoto da ke makwabtaka da Jamhuriyar Nijar, Gwamnan ya nuna rashin jin dadinsa kan asarar rayuka da dukiyoyi da aka yi, ya kuma yaba wa jami’an tsaro da suka yi iya kokarinsu wajen ganin an shawo kan lamarin, ya kuma bukaci jama’a da su rika kai rahoton duk wani motsi da suka samu ga hukuma domin daukar matakin da ya dace.

 

Tun da farko Shugaban Karamar Hukumar Arewa Alhaji Sani Aliyu ya godewa Gwamnan bisa daukar matakin gaggawa don ganin an shawo kan wannan mummunan lamari.

 

Shugaban ya kuma bayyana cewa an bayar da agajin ga wadanda abin ya shafa, inda ya ce iyalan kowannen wadanda suka rasa rayukansu sun samu Naira 500,000 yayin da kowanne daga cikin wadanda suka jikkata kuma ya samu N500,000.

 

A ranar Lahadin da ta gabata ne ‘yan bindigar Lakurawa suka kai hari kauyuka 7 a karamar hukumar Arewa ta jihar Kebbi inda suka kashe sama da mutane 10 tare da kona gidaje da dama wanda hakan ya kasance harin ramuwar gayya biyo bayan kashe wani shugabansu mai suna Maigemu da jami’an tsaro suka yi.

 

 

Abdullahi Tukur

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Gwamna Lakurawa

এছাড়াও পড়ুন:

Jihar Jigawa Za ta Kashe Sama da Naira Biliyan Daya Domin Inganta Ayyukan Wutar Lantarki

Daga Usman Muhammad Zaria

Majalisar Zartarwa ta Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Biliyan daya da miliyan dari uku domin gyara da inganta tsofaffin ayyukan wutar lantarki a fadin jihar.

Kwamishinan yada labarai, matasa, wasanni da al’adu na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed, ne ya bayyana haka ga manema labarai a Dutse.

A cewarsa, wannan mataki na daga cikin jajircewar gwamnatin Malam Umar Namadi wajen inganta samar da wutar lantarki da kuma bunkasa ci gaban al’umma musamman a yankunan karkara.

A cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai bayan zaman majalisar, Alhaji Sagir Musa Ahmed ya kara da cewa, aikin na nuna kudirin gwamnatin jihar na tabbatar da karin samun wutar lantarki, kara habakar tattalin arziki, da inganta rayuwar jama’a a birane da karkara.

Ya bayyana cewa, aikin zai kunshi samarwa da girka sabbin na’urorin bada wuta (transformers), hada garuruwa ta hanyar layin wuta na 33KV, da kuma maye gurbin turakun wuta da suka lalace a sassa daban-daban na jihar.

Sanarwar ta kara da cewa, garuruwan da za su amfana sun hada da Madaka a Gagarawa, Bosuwa a Maigatari, Mai Tsamiya da Unguwar Gawo a Sule-Tankarkar, Yandamo a Gumel, Farin a Dutse, Giginya a Gwaram, Kwanar Dindu zuwa Bulangu a Kafin Hausa, Kanya Babba a Babura da kuma Garki a Karamar Hukumar Garki.

Ya ce wannan aikin da aka yi na nuna jajircewar gwamnatin Namadi wajen samar da ci gaba mai dorewa da tabbatar da cewa kowace al’umma ta amfana da romon dimokuradiyya.

Alhaji Sagir ya kara da cewa, gwamnatin Namadi ta kuma amince da bayar da kwangilar gina rijiyoyin samar da ruwa da ke aiki da hasken rana domin sabbin gidaje na Danmodi Housing Estates.

Wadannan gidaje sun hada da na Birnin Kudu, Kafin Hausa, Kazaure, Ringim da kuma hanyar Nguru–Hadejia.

Kwamishinan ya bayyana cewa, kwangilar da ta kai fiye da Naira miliyan 378 tana nuna jajircewar gwamnatin jihar wajen samar da muhimman abubuwan more rayuwa da ke kara ingancin zama da dorewar sabbin gidaje a fadin jihar.

Ya ce amincewar wannan aiki na nuna yadda gwamnatin Namadi ke aiwatar da tsare-tsaren ci gaba cikin tsari guda, wanda ya hada da gidaje, ruwa, da makamashi mai sabuntawa domin inganta rayuwar al’umma baki daya.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutum ɗaya ya rasu yayin da ’yan sanda da ’yan bindiga suka yi artabu a Kwara
  • Kotu ta sake hana PDP gudanar da babban taronta na ƙasa
  • Tinubu ya sake naɗa Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA
  • Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci
  • Dalilin da ya kamata PDP ta jingine taron da za ta gudanar— Saraki
  • Jihar Kwara Ta Jaddada Kudirin Tallafa wa Wadanda Suka Tsira Daga Cin Zarafin Jinsi
  • Matasa 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana
  • Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki
  • Jihar Jigawa Za ta Kashe Sama da Naira Biliyan Daya Domin Inganta Ayyukan Wutar Lantarki
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 Tare Da Sace Babur A Nasarawa