HausaTv:
2025-06-15@16:57:33 GMT

Rasha  na goyon bayan sake farfado da yarjejeniyar nukiliyar Iran

Published: 13th, March 2025 GMT

Ministan harklokin wajen Rasha, Sergei Lavrov ya ce kasarsa na goyon bayan sake farfado da yarjejeniyar farko ta Iran da kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya amince da shi.

Mista Lavrov ya jaddada goyon bayan Moscow ga sake farfado da muhimmiyar yarjejeniya da Iran da manyan kasashen duniya suka rattabawa hannu a shekarar 2015.

“Mun tattauna halin da ake ciki a yankin Tekun Fasha da kuma shirin hadin gwiwa,” in ji Lavrov a wata hira, a cewar kamfanin dillancin labarai na Tass, yayin da yake amsa tambaya kan ko batun Iran na cikin tattaunawar da ake yi tsakanin Rasha da Amurka.

Rasha ta tattauna halin da ake ciki dangane da yarjejeniyar da Iran ta kulla da Amurka yayin da ta ci gaba da tattaunawa kan batun da kasashen Turai, yana mai jaddada maido da yarjejeniyar da ake yi a halin yanzu “wanda Amurkawa suka balle a lokacin gwamnatin Trump ta farko.” »

Lavrov ya bayyana cewa “Rasha za ta goyi bayan ci gaba da tsarin da ya samar da ainihin yarjejeniyar da kwamitin sulhu da Iran suka amince da ita. »

“Za mu ga yadda lamarin zai kasance,” in ji shi, yayin da yake magana kan shawarwarin da ya yi da jami’an Amurka da na Turai.

Ministan harkokin wajen na Rasha ya kuma yi magana kan rahotannin kafafen yada labaran kasashen yammacin duniya da ke nuni da cewa shugaban Amurka Donald Trump ya yi kira da a kulla sabuwar yarjejeniyar nukiliya a wata wasika da ya aike zuwa Tehran.

“Amurka na son sabuwar yarjejeniyar nukiliya da Iran don tilasta mata kada ta goyi bayan kungiyoyin da ke gabas ta tsakiya, amma wannan zabin ba zai yi tasiri ba. “Abin damuwa ne yadda Amurkawa su sanya sharuddan siyasa ga wannan sabuwar yarjejeniya,” in ji shi.

Lavrov ya kuma yi watsi da duk wani matsin lamba ga Iran kan tasirin da take da shi a yammacin Asiya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: da yarjejeniyar

এছাড়াও পড়ুন:

Iran : Halin da ake ciki ba zai iya bada damar tattaunawa da Amurka ba

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran, Esmail Baghaei, ya zargi Isra’ila da yin zagon kasa ga diflomasiyya ta hanyar tsallaka jajayen layukan kasar Iran, da kuma ta’azzara rikici da kasashen yammacin duniya, yana mai bayyana cewa, ba za a iya yin shawarwari a halin da ake ciki ba.

Sanarwar dai na nuni da koma baya sosai a yunkurin diflomasiyya na Iran da kasashen Yamma, musamman yadda tashe-tashen hankula ke kara ta’azzara bayan matakin sojin Isra’ila.

Matakin na Isra’ila da hadin kai tare da Amurka na a matsayin kokari na kawar da duk wata dama ta cimma sakamakon shawarwari.

“Ba za a iya shawarwarin ba yayin da a lokaci guda ake barin gwamnatin kisan kare dangi ta kai hari kan Iran.”

“Ba Isra’ila za ta aikata irin wadannan laifuka ba tare da amincewar Amurka ba.”

Iran dai na kallon hare-haren da Isra’ila ta kai a baya-bayan nan a matsayin wani hari kai tsaye ga ‘yan kasarta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yarima Mai Jiran Gadon Saudiyya Ya Jaddada Goyon Bayan Kasarsa Ga Iran
  • Kungiyar Abokan Yarjejeniyar M.D.D Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ke Kai Wa Kan Iran
  • Martanin sojojin Iran ga Isra’ila zai zama mafi muni idan aka ci gaba da kai hari (Pezeshkian)
  • An Yi Zanga-zangar Nuna Goyon Baya Ga Kin Amincewa Da Bakin Haure A Amurka 
  • Wakilin Sin A IAEA Ya Yi Tir Da Harin Isra’ila Kan Cibiyoyin Sarrafa Nukiliyar Iran
  • Sudan Ta Zargi Janar Haftar Na Libiya Da Goyon Bayan ‘Yan Tawayen Kasarta Na Rapid Support Forces
  • Iran : Halin da ake ciki ba zai iya bada damar tattaunawa da Amurka ba
  • Masana Ilimin Nukiliyar Iran Sun Yi Shahada
  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8
  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawa guda bayan kwanaki 8