Aminiya:
2025-07-09@07:45:48 GMT

PDP ta sake ɗage babban taronta zuwa Mayun 2025

Published: 9th, March 2025 GMT

Babbar jam’iyyar adawa ta PDP ta sake ɗage babban taronta na ƙasa (NEC), zuwa ranar 15 ga watan Mayu, 2025.

A wata sanarwa da jam’iyyar ta fitar, wanda babban sakatarenta, Sunday Ude-Okoye, ya bayyana hakan.

Iyalan Abacha sun gargaɗi Babangida kan ɓata sunan mahaifinsu An samu tsohon shugaban hukumar tsaron Faransa da zamba

Tun asali, an tsara gudanar da taron ne a ranar 13 ga watan Maris 2025, amma aka ɗage shi saboda wasu zaɓukan cike gurbi da aka gudanar a jihohi daban-daban.

Tun a shekarar da ta gabata ne PDP ta tsara yin wannan babban taro karo na 98, amma ana ci gaba da ɗagewa.

Rahotanni na nuni da cewa matsalolin cikin gida da jam’iyyar ke fuskanta, kamar rikicin shugabanci da rashin daidaiton ra’ayi tsakanin manyan jiga-jiganta, na iya zama dalilin jinkirin.

Yanzu haka, ana sa ran taron zai kasance muhimmin mataki ga makomar jam’iyyar, musamman duba da shirye-shiryenta na fafatawa a babban zaɓen 2027.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Babban taro jam iyya Siyasa taro

এছাড়াও পড়ুন:

 Togo: An Yi Kiran Sake Yin Wata Sabuwar Zanga-zanagr Kin Jinin Gwamnati

Kungiyoyi farar da jam’iyyun adawar  siyasa a kasar Togo, sun sake yin kira da a gudanar da Zanga-zanga a ranar 16 da 17 ga watan nan na Yuli da ake ciki.

Masu Zanga-zangar dai suna son nuna kin amincewa ne da siyasar hukumar kasar da suke bayyanawa da ta kama-karya, haka nan kuma kashe wasu mutane da aka yi a Zanga-zangar da ta gabata.

Bugu da kari, kiran a yi zanga-zangar dai ya zo ne bayan kama wasu ‘yan hamayyar siyasa da aka yi da kuam kara kudin wutar lantarki, da amince da sabon tsarin mulki da ya kara bai wa shugaban kasar Faure Gnassingbe karfin iko.

Wasu fitattun masu fafutuka a kasar, sun watsa sanarwa a shafukan sada zumunta da a cikin suke yin kiran mutane su fito domin yin Zanga-zangar ta wannan watan na Yuli.

Zanga-zangar karshe da aka yi a kasar, ta yi sanadiyyar mutuwar mutane 7 kamar yadda majiyar masu fafutukar ta ambata, sai dai kuma mahukuntan kasar sun ce, mutane biyu ne kadai su ka rasa rayukansu, kuma nustewa su ka yi a ruwa.

Har ila yau majiyar ‘yan hamayyar ta ce, an kame mutane da adadinsu ya kai 60 a yayin waccan Zanga-zangar.

A ranar 17 ga watan Yuli ne ake sa ran yin zaben kananan hukumomi, da jam’iyyun hamayya suke yin kira da a dage zaben zuwa wani lokaci a can gaba, har yanyin siyasar kasar ya bayar da dama.

A gefe daya, jam’iyyar da take Mulki a kasar ta dage taron da ta shirya yi a wannan Asabar din mai zuwa domin nuna goyon bayanta ga shugaban kasa, ba tare da bayyana dalilin yin hakan ba, kamar yadda kamfanin dillancin labarun Faransa ya nakato.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820
  • An ƙayyade maki da shekarun shiga jami’a a Nijeriya
  • Kotu Ta Ɗage Yanke Hukunci Kan Neman Izinin Jinyar Yahaya Bello
  • ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni
  • NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19
  •  Togo: An Yi Kiran Sake Yin Wata Sabuwar Zanga-zanagr Kin Jinin Gwamnati
  • Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC
  • Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum
  • Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha
  • Kofin Duniya: Real Madrid Za Ta Fara Da PSG A Semi Final