Aminiya:
2025-03-16@01:14:09 GMT

PDP ta sake ɗage babban taronta zuwa Mayun 2025

Published: 9th, March 2025 GMT

Babbar jam’iyyar adawa ta PDP ta sake ɗage babban taronta na ƙasa (NEC), zuwa ranar 15 ga watan Mayu, 2025.

A wata sanarwa da jam’iyyar ta fitar, wanda babban sakatarenta, Sunday Ude-Okoye, ya bayyana hakan.

Iyalan Abacha sun gargaɗi Babangida kan ɓata sunan mahaifinsu An samu tsohon shugaban hukumar tsaron Faransa da zamba

Tun asali, an tsara gudanar da taron ne a ranar 13 ga watan Maris 2025, amma aka ɗage shi saboda wasu zaɓukan cike gurbi da aka gudanar a jihohi daban-daban.

Tun a shekarar da ta gabata ne PDP ta tsara yin wannan babban taro karo na 98, amma ana ci gaba da ɗagewa.

Rahotanni na nuni da cewa matsalolin cikin gida da jam’iyyar ke fuskanta, kamar rikicin shugabanci da rashin daidaiton ra’ayi tsakanin manyan jiga-jiganta, na iya zama dalilin jinkirin.

Yanzu haka, ana sa ran taron zai kasance muhimmin mataki ga makomar jam’iyyar, musamman duba da shirye-shiryenta na fafatawa a babban zaɓen 2027.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Babban taro jam iyya Siyasa taro

এছাড়াও পড়ুন:

Hamas Tace A Shirye Take Ta Sake Fursinonin HKI Da Amurka, Tare Da Gawaki Wasu Guda 4

Kungiyar Hamas wacce take iko da zirin gaza na kasar Falasdinu da aka mamaye ta bada sanarwan cewa a shirye take da saki fursinonin HKI da Amurka, har ma da gawakin wasu 4, idan HKI ta dawo kan ci gaba da aiwatar da abubuwan da yarjeniyar tsagaita wuta a tsakaninta da HKI.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto wani Jami’in kungiyar yana fadar haka a jiya Jumma’a. Ya kuma kara da cewa, wasu daga cikin wadanda suke tsakanin kungiyar da HKI ne ya bata wannan shawarar, sannan ya kara da cewa, sai dai wannan matakin yana da sharudda, kuma sune HKI ta amince ta dawo kan tattaunawa marhala ta biyu don aiwatar da yarjeniyar da aka cimma tsakanin bangarorin biyu.

Taher al-Nounou ya fadawa kamfanin dillancin labaran AFP na kasar Faransa kan cewa Hamas zata salami Edan Alexander wanda yake dauke da passport na Amurka da kuma wasu 4 wadanda suke dauke da Passport na kasashen biyu wato HKI da kuma Amurka. Amma tare da wannan sharadin.

Sanarwan ta kammala da cewa kungiyar ta fara sabuwar tattaunawa a birnin Doha na kasar Qatar a ranar Talatan da ta gabata sannan tawagar HKI ma tana halattar tattaunawan wand aba kai tsaye ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fitar Da Nama Zuwa Saudiyya: Mayankar Dabbobi Ta Jurassic Ta Yi Hadin-gwiwa Da Shirin CDI
  • Hamas Tace A Shirye Take Ta Sake Fursinonin HKI Da Amurka, Tare Da Gawaki Wasu Guda 4
  • Birnin Beijing Ya Shirya Yiwa ‘Yan Mata Rigakafin Cutar HPV Kyauta
  • MC Tagwaye ya fice daga APC zuwa SDP
  • An Cire Maguire Cikin Tawagar Ingila Da Za Ta Buga Wasan Neman Gurbi
  • Hajjin Bana: NAHCON Za Ta Fara Jigilar Maniyyata A Ranar 6 Ga Mayu
  • Ranar Mata Ta Duniya: Kalubalen Da Mata Ke Fuskanta A Siyasar Nijeriya
  • FERMA Ta Sake Jaddada Sadaukarwar Da Take Yi Na Kula Da Hanyoyin Tarayya
  • An Bada Umarnin Sake Tsugunar Da Wadanda Harin ‘Yan Bindiga Ya Rutsa Da Su A Kebbi
  • Rasha  na goyon bayan sake farfado da yarjejeniyar nukiliyar Iran