Kungiyar Hamas wacce take iko da Zirin Gaza ta bada sanarwan cewa an kawo karshen takaddama da HKI dangane da jinkirin da tayi wajen sakin fursinonin Falasdinawa 620 a ranar Asabar da ta gabata bayan da ta saki fursinoni yahudawa har 6.

Tashar talabijin ta Prersstv a nan Tehran ta nakalto kakakin kungiyar Hazem Qassem yana fadar haka a yau Laraba, ya kuma kara da cewa, gwamnatin kasar Masar ce mai shiga tsakani, kuma ta lamuncewa kungiyar kan cewa shirin musayar zai sake komawa kan yadda aka tsara shi, sannan HKI zata sake wadannan fursinoni Falasdinawa.

Banda haka labarin ya kara da cewa a gobe Alhamis ma kungiyar Hamas zata mika gawakin yahudawa 4 wadanda take tsare da su a hannunta tun cikin yakin tufanul Aksa.

A Zagaye na farko na musayar fursinonin tsakanin Hamas da HKI dai, Hamas ta sake yahudawa 33, a yayinda yahudawan suka saki fursinoni falasdinawa kimani 2000.

Marhala ta karshe bayan musayar fursinoni da gawawwaki shi ne, janyewar sojojin HKI daga zirin gaza, ko yankin philidelpia  da kuma maganar sake gina gaza. Bayan da HKI ta rusa gine-gine har 170,000 a cikin shekara guda da watanni 3.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka ta sake yin watsi da kiran tsagaita a wuta Gaza

Amurka ta sake hana kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya kiran tsagaita bude wuta da kuma kai agajin jin kai a Gaza.

Wannan hawa kujerar na-ki shi ne irinsa na farko na sabuwar gwamnatin Trump kuma yana zuwa ne a daidai lokacin da Isra’ila ke fuskantar matsin lamba daga kasashen duniya kan ci gaba da yakin da takeyi a gaza dama hana shigar da kayan agaji.

Daftarin kudurin da aka gabatar wa kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya a ranar Laraba ya bukaci “a gaggauta tsagaita wuta na dindindin” da kuma sakin wadanda aka yi garkuwa da su ba tare da wani sharadi ba.

Kudirin da kasashe 10 wadanda ba mambobin kwamitin na dindindin ba suka gabatar, ya samu sahalewa daga kasashe 14, yayin da Amurka ta yi fatali da shi.

Kafin kada kuri’ar, Amurka ta ce “kudirin zai wargaza kokarin diflomasiyya na cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta gaskiya, kuma zai karfafa wa Hamas,” ne in ji jakadiyar Amurka a Majalisar Dinkin Duniya, Dorothy Shea.

Jakadan Falasdinawa a Majalisar Dinkin Duniya Riyad Mansour ya bukaci MDD da ta dauki mataki.

Wannan matakin na ranar Laraba ya kasance karo na shida da Amurka ke toshe kudurin tsagaita wuta a Gaza tun watan Oktoban shekarar 2023.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
  • Gwamna Uba Sani Ya Samu Goyon Bayan Mazauna Mahuta Bayan Warware Rikicin Filaye
  • Araghchi : Babu wata tattaunawa idan ba zamu tace uranium ba
  • Amurka ta sake yin watsi da kiran tsagaita a wuta Gaza
  • Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kashe Falasdinawa Wadanda Suke Jin Yunwa A Gaza
  • Ba zan yi musayar yawu da yara ba — Martanin Amaechi ga Wike
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Jaddada Hakkin Iran Na Tace Sinadarin Uranium
  • Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG
  • Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva
  • Nasarorin Shekaru Biyun Tinubu Shaida Ne Ta Shugaba Mai Hangen Nesa – Ministan Yada Labarai