HausaTv:
2025-11-03@10:04:39 GMT

                          Me Turkiya Take So A Syria?

Published: 26th, February 2025 GMT

 A farko-farkon da masu dauke da makamai su ka kwace iko da birnin Halab, jami’an gwganatin Turkiya sun kaucewa yin Magana akan abinda yake faruwa.

Sa dai kuma da yake mai kaza a aljihu ba ya jimirin cas, ba a je ko’ina ba, su ka fara furta kalaman da suke nuni da cewa, Da kawai rina a kaba. Ministan harkokin wajen Turkiya Hakan Fidan, ya yi tsokaci akan abinda yake faruwa a Syria, ya zargi  tsohuwar gwamnatin Syria da cewa; Ba ta yi aiki da bangarorin yarjejeniyar Astana ba.

Sojojin Turkiya suna cikinm kasar Syria tun a farkon 2018, inda suke mamaye da kaso 10% na yankin wannan kasa. Kuma aiki a tare da masu adawa da gwamnatin Damascuss,musamman rundunar da ake kira da             “ Sojojin Kasar Syria” wacce aka kafa  a cikin garin Orfa a ranar 4 ga watan Oktoba na shekarar 2019. Kafa wannan rundunar ya kasance kwanaki kadan gabanin hasken da Amurka da Rasha su ka bai wa Turkiyan ta kai wa Kurdawa hari a gabashin tekun Euphrates.

 Turkiya din ce take bai wa wannan runudnar makami da kudi da albashi da dukkanin abinda suke bukata domin maye gurbin rundunar “ Free Syrian Army” wacce ita ma a cikin kasar Turkiya aka kafa ta a  watan Ogusta na 2011.

 Kafafen watsa labarun Turkiya suna kaucewa ambaton rawar da gwamnatin kasar tasu take takawa a cikin abubuwan da suke faruwa a cikin Syria. Abinda suke cewa shi ne: “ Rundunar ‘yan adawa ta Syria”, ko kuma su kira su da “ Masu adawa da Assad.” Haka nan kuma suna kiransu da |Rundunar Hatsh” ba tare da sun fayyace abinda wadannan haruffan  hudu suke nufi ba da kuma alakarta da rundunar; Jubhatun-Nusrah’. Wannan kungiyar kuwa sunanta ta ‘yan ta’adda a bisa dokar da shugaban Turkiya Urdugan ya rattabawa hannu a ranar 29 ga watan Ogusta na 2018.

Kafafen watsa labarun gwamnati na Turkiya ba su Magana akan alakar da take a tsakanin rundunar  Jaisuhl Watani al-Suri”da kuma |Hay’atult-tahirish-sham.” da suke a cikin garin Idlib, kuma Turkiyan ce ta rika ba su dukkanin abubuwan da suke bukatuwa da su na man fetur, wutar lantarki, ruwa, internet, da dukkanin hajar da ake amfani da ita ta yau da kullum. Tsakanin iyakar Turkiya zuwa Idlib, kilo  mita 40 ne kadai.Bugu da kari ana kashe kudaden Turkiya a cikin wannan yankin na Idlib. Haka nan kuma babu wata hanyar da za iya shiga cikinsa sai ta hanyar Turkiya, wato dai a fakaice za a iya cewa, an yanke wanann yankin da Syria ya zama wani bangare na Turkiya.

Bayan wannan, kafafen watsa labarun na Turkiya sun rika Magana akan muhimmancin  da garin Halab yake da shi a wurin Turkiya, ko da kuwa na wucin gadi ne. Hakan ta faru ne bayan da rundunar “Jaishul Watani al-Suri” ya kwace iko da garin Tal-Rif’ da kuma korar  mayakan Kurdawa daga cikinsa, haka nan wasu unguwanni a cikin birnin na Halab.

Kurduwan dai sun shimfida ikonsu ne a cikin wadannan yankunan bisa yarjejeniya da  tsohuwar gwamnatin Damascuss.

Kafafen watsa labarun na Turkiya sun rika bayyana abinda ya faru da cewa, bugu ne mai kyau da aka yi wa Kurdawa da kawo musu cikas, a kokarin da suke yin a kafa yankinsu mai cin gashin kansa a cikin Syria. Haka nan kuma kafafen watsa labarun ta Turkiya sun rika yi wa Kurdawan barazana cewa sojoji za su mamaye gabashin tekun “Eupherate” da can ne cibiyar kurdawan idan an gama da ‘yantar da dukkanin Syria da kifar da gwamnatin Asad.

 Bugu da kari, kafafen watsa labarun Turkiyan sun rufe idanunsu akan yadda  daruruwan masu dauke da makamai da su ka shiga cikin birnin Halab, suke Magana da harshen turkanci da Karin harshe irin an Uzabakistan, Shishan, da Kuma Egoz na kasar China.

 **

Wani abu da ya fi bayar da mamaki shi ne yadda wasu Turkawa, su ka fara cewa, ai dama gundumar Halab, ta turkiya ce, domin tana a karkashin Daular Usmaniyya har zuwa 1918, an kuma kori Turkawa daga ciki ne bayan da aka yi galaba akan Daular Usmaniyya a yakin duniya na farko.

Wannan labarin na Turkiya, ya yi kama da abinda Turkawan su ka rika fada a lokacin abinda aka kira da “Yunkurin Larabawa” a 2011 da su ka rika yin bore a cikin kasashe mabanbanta domin samun ‘yanci. A wancan lokacin Turkawan sun rika cewa, yankunan Halab, Idlib, Riqqah, Deir-zur, da kuma arewacin Iraki wato Mausel,  Karkuk da Arbil da Sulaimaniyya, duk wani yanki ne na Turkiya. Wasu kuma sun rika cewa, Idlib ce jahar Turkiya ta 81.

 Bugu da kari an rika ganin hotuna da tutocin Turkiya akan ginin “Wani tsohon gini mai tarihi na garin Halab.

A ranar Talata 10 /12/2024 shugaban kungiyar kishin turkancin “Daulat Bahshali “ya bayyana cewa” Halab Gari ne na Turkawa.”

Loakcin da ‘yan tawayen masu dauke da makamai suke shirin shiga garin Halab, Turkiya ta umarce su da kar su cutar da mazaunasa domin ba ta damar aiwatar da shirinta na tattalin arziki wanda ya kunshi, ba su wutar lantarki, man fetur da dukkanin hajojin da suke da bukatuwa da su. Wanann shi ne abinda Turkiyan ta tsara a tsawon shekaru 13 na yaki.

Ankara ta so ganin cewa duk inda  ‘yan tawaye su ka shiga su yi kyakkyawar mu’amala da mutane, saboda ita kuma ta ci moriyar hakan ta fuskar tattalin ariziki.

A karshe kuwa, mayakan sun shiga birnin Damscuss, inda su ka zama gwaraza, sannan kuma Turkiya ta zama wata gwarzuwa da kuma a nan gaba za ta ci moriyar taimakawa ‘yan adawa na shekaru masu tsawo, ta fuskokin siyasa da tattalin arziki.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa

Manajar  ofishin na NIWA,  da ke a jihar ta Legas Injiniya Sarat Braimah ta bayyana cewa, tura ma’ikatan hukumar domin yin aikin, zai taimaka wajen gudanar da aikin a cikin inganci.

Kazalika, ya sanar da cewa, hakan zai kuma bayar da damar yin safarar kaya a cikin sauki da kuma safarar matafiya da ke bin hanyar ruwa ta yankin na Ikorodu.

“Mun yi nazari a cikin kwanciyar hankali kan yadda za a tabbatar da an cire fulawar da ke a cikin kasan ruwan ba tare da wata miskila ba tare da kuma bai wa jiragen ruwan damar yin zirga-zirgarsu a hanyoyin ruwan, ba tare da wata matsala ba, “ Inji Injiya Braimah.

“ Aikin ya wuce batun fannin samar da saukin yin sufurin jiragen ruwan har da tabbatar da an kiyaye janyo matsala ga ayyukan kamun Kifi a hanyoyin na ruwan, “ A cewar Inji Manajar.

Ta kara da cewa, babban shugabanmu na hukumar ta NIWA,  Bola Oyebamiji, ne tuni ya riga ya bayar da kwangilar yin aikin, ba wai a jihar Legas kawai ba, har da a sauran hanyoyin ruwa  da ke a sassan kasar.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka November 2, 2025 Labarai Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala November 2, 2025 Manyan Labarai An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano November 2, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ummar Kauru Sun Koka Game Da Karuwar Hare-hare Da Ke Barazana Ga Gonaki Da Rayuka
  • Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
  • Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka
  • Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu
  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  • Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • Amurka ta sanya Najeriya cikin ƙasashen da ake yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi
  • Za mu ci gaba da shirye-shiryen babban taronmu — PDP
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar