A farko-farkon da masu dauke da makamai su ka kwace iko da birnin Halab, jami’an gwganatin Turkiya sun kaucewa yin Magana akan abinda yake faruwa.
Sa dai kuma da yake mai kaza a aljihu ba ya jimirin cas, ba a je ko’ina ba, su ka fara furta kalaman da suke nuni da cewa, Da kawai rina a kaba. Ministan harkokin wajen Turkiya Hakan Fidan, ya yi tsokaci akan abinda yake faruwa a Syria, ya zargi tsohuwar gwamnatin Syria da cewa; Ba ta yi aiki da bangarorin yarjejeniyar Astana ba.
Sojojin Turkiya suna cikinm kasar Syria tun a farkon 2018, inda suke mamaye da kaso 10% na yankin wannan kasa. Kuma aiki a tare da masu adawa da gwamnatin Damascuss,musamman rundunar da ake kira da “ Sojojin Kasar Syria” wacce aka kafa a cikin garin Orfa a ranar 4 ga watan Oktoba na shekarar 2019. Kafa wannan rundunar ya kasance kwanaki kadan gabanin hasken da Amurka da Rasha su ka bai wa Turkiyan ta kai wa Kurdawa hari a gabashin tekun Euphrates.
Turkiya din ce take bai wa wannan runudnar makami da kudi da albashi da dukkanin abinda suke bukata domin maye gurbin rundunar “ Free Syrian Army” wacce ita ma a cikin kasar Turkiya aka kafa ta a watan Ogusta na 2011.
Kafafen watsa labarun Turkiya suna kaucewa ambaton rawar da gwamnatin kasar tasu take takawa a cikin abubuwan da suke faruwa a cikin Syria. Abinda suke cewa shi ne: “ Rundunar ‘yan adawa ta Syria”, ko kuma su kira su da “ Masu adawa da Assad.” Haka nan kuma suna kiransu da |Rundunar Hatsh” ba tare da sun fayyace abinda wadannan haruffan hudu suke nufi ba da kuma alakarta da rundunar; Jubhatun-Nusrah’. Wannan kungiyar kuwa sunanta ta ‘yan ta’adda a bisa dokar da shugaban Turkiya Urdugan ya rattabawa hannu a ranar 29 ga watan Ogusta na 2018.
Kafafen watsa labarun gwamnati na Turkiya ba su Magana akan alakar da take a tsakanin rundunar Jaisuhl Watani al-Suri”da kuma |Hay’atult-tahirish-sham.” da suke a cikin garin Idlib, kuma Turkiyan ce ta rika ba su dukkanin abubuwan da suke bukatuwa da su na man fetur, wutar lantarki, ruwa, internet, da dukkanin hajar da ake amfani da ita ta yau da kullum. Tsakanin iyakar Turkiya zuwa Idlib, kilo mita 40 ne kadai.Bugu da kari ana kashe kudaden Turkiya a cikin wannan yankin na Idlib. Haka nan kuma babu wata hanyar da za iya shiga cikinsa sai ta hanyar Turkiya, wato dai a fakaice za a iya cewa, an yanke wanann yankin da Syria ya zama wani bangare na Turkiya.
Bayan wannan, kafafen watsa labarun na Turkiya sun rika Magana akan muhimmancin da garin Halab yake da shi a wurin Turkiya, ko da kuwa na wucin gadi ne. Hakan ta faru ne bayan da rundunar “Jaishul Watani al-Suri” ya kwace iko da garin Tal-Rif’ da kuma korar mayakan Kurdawa daga cikinsa, haka nan wasu unguwanni a cikin birnin na Halab.
Kurduwan dai sun shimfida ikonsu ne a cikin wadannan yankunan bisa yarjejeniya da tsohuwar gwamnatin Damascuss.
Kafafen watsa labarun na Turkiya sun rika bayyana abinda ya faru da cewa, bugu ne mai kyau da aka yi wa Kurdawa da kawo musu cikas, a kokarin da suke yin a kafa yankinsu mai cin gashin kansa a cikin Syria. Haka nan kuma kafafen watsa labarun ta Turkiya sun rika yi wa Kurdawan barazana cewa sojoji za su mamaye gabashin tekun “Eupherate” da can ne cibiyar kurdawan idan an gama da ‘yantar da dukkanin Syria da kifar da gwamnatin Asad.
Bugu da kari, kafafen watsa labarun Turkiyan sun rufe idanunsu akan yadda daruruwan masu dauke da makamai da su ka shiga cikin birnin Halab, suke Magana da harshen turkanci da Karin harshe irin an Uzabakistan, Shishan, da Kuma Egoz na kasar China.
**
Wani abu da ya fi bayar da mamaki shi ne yadda wasu Turkawa, su ka fara cewa, ai dama gundumar Halab, ta turkiya ce, domin tana a karkashin Daular Usmaniyya har zuwa 1918, an kuma kori Turkawa daga ciki ne bayan da aka yi galaba akan Daular Usmaniyya a yakin duniya na farko.
Wannan labarin na Turkiya, ya yi kama da abinda Turkawan su ka rika fada a lokacin abinda aka kira da “Yunkurin Larabawa” a 2011 da su ka rika yin bore a cikin kasashe mabanbanta domin samun ‘yanci. A wancan lokacin Turkawan sun rika cewa, yankunan Halab, Idlib, Riqqah, Deir-zur, da kuma arewacin Iraki wato Mausel, Karkuk da Arbil da Sulaimaniyya, duk wani yanki ne na Turkiya. Wasu kuma sun rika cewa, Idlib ce jahar Turkiya ta 81.
Bugu da kari an rika ganin hotuna da tutocin Turkiya akan ginin “Wani tsohon gini mai tarihi na garin Halab.
A ranar Talata 10 /12/2024 shugaban kungiyar kishin turkancin “Daulat Bahshali “ya bayyana cewa” Halab Gari ne na Turkawa.”
Loakcin da ‘yan tawayen masu dauke da makamai suke shirin shiga garin Halab, Turkiya ta umarce su da kar su cutar da mazaunasa domin ba ta damar aiwatar da shirinta na tattalin arziki wanda ya kunshi, ba su wutar lantarki, man fetur da dukkanin hajojin da suke da bukatuwa da su. Wanann shi ne abinda Turkiyan ta tsara a tsawon shekaru 13 na yaki.
Ankara ta so ganin cewa duk inda ‘yan tawaye su ka shiga su yi kyakkyawar mu’amala da mutane, saboda ita kuma ta ci moriyar hakan ta fuskar tattalin ariziki.
A karshe kuwa, mayakan sun shiga birnin Damscuss, inda su ka zama gwaraza, sannan kuma Turkiya ta zama wata gwarzuwa da kuma a nan gaba za ta ci moriyar taimakawa ‘yan adawa na shekaru masu tsawo, ta fuskokin siyasa da tattalin arziki.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
Sojoji biyu sun ji rauni bayan wani harin kwanton baya da ’yan bindiga suka kai kan ayarin motocin Kwamandan kwamandan Rundunar Sojoji ta 382 Ƙaramar Hukumar Faskari ta jihar Katsina.
Lamarin ya faru ne a ƙauyen Ruwan Godiya, kan hanyar Sheme–Kankara, lokacin da tawagar Operation Fansan Yamma (OPFY) ke wucewa.
Ganau sun ce sojojin na kan hanyar ziyartar sansanonin sojoji a yankunan Faskari da Mabai da Ɗan Ali lokacin da aka kai musu hari.
Sai dai sun yi nasarar tunkarar ’yan bindigar har suka kuvuta, kodayake sojoji biyu sun samu raunuka na harbi kuma aka kai su asibitin sojoji domin jinya.
An kai wa sojojin harin ne a rana ɗaya da shugabannin al’ummar Faskari suka zauna da wakilan ’yan bindiga domin rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya.
’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBSHakan ya sanya Faskari zama ƙaramar hukuma ta baya-bayan nan da ta shiga irin wannan sulhu bayan ƙananan hukumomin Ɗanmusa da Jibia, Batsari da Ƙanƙara, Kurfi da Musawa.
Yarjejeniyar na neman kawo ƙarshen tashin-tashina, garkuwa da mutane da kuma ƙaura da ake fama da su a jihar.
Amma akwai shakku kan ɗorewar ta, domin wasu daga cikin shugabannin ’yan bindigar sun bayyana cewa sulhun ya shafi ƙananan hukumomin da suka shiga yarjejeniyar kawai, lamarin da ya janyo tsoron cewa sauran wuraren da ba su rattaba hannu ba, suna iya ci gaba da fuskantar hare-hare.
Wasu mazauna Ruwan Godiya sun ce ayyukan ’yan bindiga na ƙara ta’azzara a sassan Katsina duk da yarjejeniyar sulhun da aka ƙulla da wasu daga cikin shugabanninsu.
Masana sun bayyana cewa hakan ya nuna raunin irin waɗannan tsare-tsare na sulhu, tare da tabbatar da buƙatar ƙarin sa-ido a yankunan da ke fuskantar barazana.
Sulhun Faskari da ’yan bindigaƘaramar Hukumar Faskari ta zama ta baya-bayan nan a Jihar Katsina da ta shiga yarjejeniyar zaman lafiya da ’yan bindiga, domin kawo ƙarshen kashe-kashe, garkuwa da mutane da kuma ƙaura da ake fama da su a yankin.
Kamar sauran sulhunan da aka kulla a ƙananan hukumomi guda shida, sharuddan yarjejeniyar sun ba wa ’yan bindiga damar shiga garuruwa da kasuwanni da asibitoci.
Haka kuma, za su sako duk wanda aka yi garkuwa da shi ba tare da sharaɗin ba. A sakamakon haka, al’umma za su iya komawa gona da kasuwanni cikin kwanciyar hankali ba tare da fargabar farmaki ba.
Yarjejeniyar ta biyo bayan taron al’umma da aka yi a Faskari, inda fitaccen shugaban ’yan bindiga, Ado Aliero, wanda ake nema ruwa a jallo, ya tabbatar wa manoma tsaronsu.
“Daga yau kowa ya koma gona cikin kwanciyar hankali; ba abin da zai faru a Faskari baki ɗaya,” in ji Aliero cikin wani bidiyo da Aminiya ta gani.
Aliero ya ɗora laifin rushewar yarjejeniyar da aka yi a baya kan cafke ɗansa, yana mai cewa ya bi duk hanyoyin lumana, amma abin ya gagara, kafin ya koma tayar da hankali.
A wani bidiyo daban kuma, wani ɗan bindiga da aka gani sanye da rigar harsashi ya zargi hukumomi da nuna wariya da rashin adalci, yana mai cewa sulhu na gaskiya zai tabbata ne kawai idan aka yi adalci ga kowa.
Sai dai duk da rahotannin da ke cewa jami’an gwamnati da na tsaro sun halarci taron, gwamnatin Jihar Katsina ta nesanta kanta daga wannan yarjejeniyar.
Akwai masu kawo cikas — Gwamna RaɗɗaGwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Raɗɗa, ya ce duk da irin ƙalubalen tsaro da ake fuskanta, gwamnatinsa na samun ci-gaba, sai dai akwai masu ƙoƙarin kawo cikas.
Ya bayyana haka ne a wani taron shawarwari da aka gudanar a Katsina ranar Lahadi, wanda ya tattaro manyan masu ruwa da tsaki ciki har da sarakunan gargajiya da shugabannin siyasa da shugabannin tsaro da masana, ’yan kasuwa da shugabannin addini.
Gwamnan ya ce tsaro ne ginshiƙin ajandar ci-gabansa tare da ilimi da noma da kiwon lafiya da kuma tallafa wa ƙanana da matsakaitan ’yan kasuwa.
Ya sanar da cewa gwamnati za ta gina gidaje 152 ga iyalan da aka raba da muhallansu a Jibia, tare da shirya shirin tallafa wa tubabbun ’yan ta’adda da suka domin kada su koma ɓarna.
Haka kuma ya yaba wa jami’an sa-kai da ƙungiyoyin tsaro na gari da suka taimaka wajen dawo da ƙwarin gwiwa a tsakanin jama’a.
Cikin manyan da suka halarci taron akwai tsohon Gwamna Aminu Bello Masari da dattijo Sanata Abu Ibrahim da fitaccen dan kasuwa Alhaji Ɗahiru Mangal da Sarkin Daura Alhaji Faruk Umar Faruk da tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama, Hadi Sirika, Ministan Gidaje Arc. Ahmed Ɗangiwa, da kuma Hadiza Bala Usman mai ba shugaban ƙasa shawara kan tsare-tsare.
Sauran sun hada da tsohon Daraktan DSS Alhaji Lawal Daura, tsohon Daraktan NIA Ambasada Ahmed Rufai, tsohon Shugaban Kamfanin na NNPC Injiniya Abubakar Yar’adua da Babban Alƙalin jihar Alhaji Musa Ɗanladi, da kuma manyan hafsoshin soja da dama da suka yi ritaya.
Hakazalika, an samu halartar manyan jami’ai, malamai daga jami’o’i da ƙungiyoyin ƙwadago da ƙungiyoyin farar hula da ’yan kasuwa da sauran shugabanni daga sassa daban-daban na jihar.
Gwamna Radda ya jaddada cewa zai ci gaba da karɓar suka da shawarwari daga masu kishin ƙasa, tare da kira ga haɗin kai domin shawo kan matsalolin tsaro da tattalin arziki da jihar ke fama da su.
A nasa vangarenm Mataimakin Gwamnan Jihar Katsina, Faruk Lawal Joɓe, ya bayyana cewa gwamnatin Raɗɗa ta samar da sama da ayyuka 35,903 a fannoni daban-daban ta karkashin manufar “Gina Makomarka.”
Joɓe ya bayyana ce an samar da ayyukan ne ta hanyar ɗaukar malamai da shugabannin unguwanni da jami’an tsaro na sa da mafarauta da sauransu domin su riƙa taka rawa wajen wanzar da zaman lafiya.
Ya kuma yi ƙarin haske kan aikin Sabunta Birane na Katsina State Urban Renewal da ya lashe Naira biliyan 74.9 wanda ya shafi manyan ayyuka a Daura da Funtua da Katsina.
Ayyukan sun haɗa da gina sabuwar hanyar Eastern Bypass mai tsawon kilomita 24, titi mai hannu biyu a cikin Katsina, gyaran tituna a Daura da Funtua, da kuma kammala wasu muhimman hanyoyin karkara.
A nasa jawabin, Kwamishinan Tsaro na Cikin Gida, Dakta Nasir Muazu, ya ce gwamnatin Raɗɗa ta ɗauki matakin rashin tattaunawa da ’yan bindiga.
Ya ce abubuwan da ke haifar da ta’addanci sun haɗa da son zuciya da rikice-rikicen albarkatu da sauyin yanayi, da kuma rashin adalci a cikin al’umma.
Ya ƙara da cewa daga 2011 zuwa 2015 matsalar ta tsaya a ƙananan hukumomi biyar, amma ta bazu zuwa 25 a lokacin tsohon Gwamna Aminu Masari bayan shirin afuwa ya faskara.
Kwamishinan ya bayyana cewa hare-haren soji sun lalata maɓoyar ’yan bindiga da dama, sun buɗe manyan hanyoyi, sannan mutum 628 da suka tsira daga hare-hare sun samu kulawar lafiya a bana.
Ya ce yanzu dakarun Community Watch, masu aikin sa-kai da ’yan banga suna mara baya ga jami’an tsaro da ke amfani da jirage marasa matuƙa da makamai da motocin aiki.
Shugaban Ƙungiyar ƙwadago (TUC) na jihar, Muntari Abdu Ruma, ya gargaɗi gwamnati ta yi taka-tsantsan da yarjejeniyar zaman lafiya da ’yan bindiga lura da yarjejeniyar Kankara ta 2016 da ta gagara.
Haka kuma, shugaban ƙungiyoyin farar hula na jihar, Malam Abdulrahman Abdullahi, ya ce akwai buƙatar ƙarin haɗin kai tsakanin jihohin Arewa maso Yamma wajen yaki da ’yan bindiga. Ya yi nuni da cewa ziyarar da dattawan Katsina suka kai wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu a bisa jagorancin Gwamna Raɗɗa ta fara haifar da sakamako mai kyau a Ƙanƙara da Faskari, amma dole a ci gaba da ayyuka cikin tsari.
A nasa ɓangaren, Sanata Ibrahim Tsauri na jam’iyyar adawa PDP, ya ce taron ya fi karkata wajen bayyana nasarorin gwamnati fiye da ba wa mahalarta dama su yi sharhi.
Duk da haka ya ce idan aka ci gaba da irin waɗannan taruka, za su iya kawo sauyi ga jihar bayan shekaru 15 na ƙalubale.
An ce mahalarta taron sun yi alkawarin mara wa gwamnati baya wajen shawo kan matsalar samari, musamman shaye-shaye da sauran laifuka.
Sauran muhimman shawarwarin sun haɗa da haɗe hanyoyin sadarwa a wuri guda da nufin samun nasarar wannan abu da aka sanya a gaba.