An Cimma Matsaya Kan Sakin Fursunonin Falasdinawa 206 Da Isra’ila Ta Jinkirta
Published: 26th, February 2025 GMT
An cimma matsaya tsakanin Isra’ila da Hamas kan sakin fursunomin Falasdianwan nan 206 da Isra’ila ta jinkira, bayan da Hamas ta saki ‘yan Isra’ila shida.
An dai tsara sakin fursunonin a ranar Asabar data gabata, saidai Isra’ila ta jinkirta sakin falasdinawan bisa abinda ta kira rashin gamsuwa da cin wulakanta ‘yan kasarta gabanin sakin da kungiyar Hamas ke yi.
Bayanai sun ce za’a saki falasdinawan su 206 a cikin sa’o’I 24 masu zuwa.
Dangane da dakatar da sakin fursunonin, Hamas ta zargi Isra’ila da “saka dukkan yarjejeniyar tsagaita wuta a cikin hatsari mai tsanani” tare da yin kira ga kasashe masu shiga tsakani da su shiga tsakani.
A nata bangaren, Hamas za ta mika wasu gawawwakin ‘yan Isra’ila hudu da ta yi garkuwa da su.
Kuma za a yi hakan ne ba tare da wani biki ba, ba tare da shirya taron da kungiyar Hamas ta saba yi ba wajen sallamar wadanda ta yi garkuwa dasu.
Za a mika gawarwakin ne tare da kungiyar agaji ta Red Cross, amma kuma da taimakon Masar.
A cewar sojojin Isra’ila, daga cikin mutane 251 da aka yi garkuwa da su a ranar 7 ga Oktoba, 62 suka rage a Gaza, sannan 35 daga cikinsu sun mutu.
A ranar 1 ga watan Maris mai shirin kamawa ne ya kamata matakin farko na yarjejeniyar tsagaita wutar ta tsakanin Isra’ila da Hamas ta kawo karshe, domin shiga mataki na biyu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Fursunan da aka yanke wa hukuncin kisa ya tsere daga gidan yari a Yobe
Wani fursuna mai suna Abba Hassan, wanda aka yanke wa hukuncin kisa, ya tsere daga gidan gyaran hali na Potiskum da ke Jihar Yobe.
Rundunar ’yan sanda ta Jihar, ta tabbatar da wannan lamari a cikin wata sanarwa da kakakinta, DSP Dungus Abdulkarim, ya fitar a ranar Asabar.
Tinubu ya yanke hulɗa da Amurka kawai — Sheikh Gumi Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan AmurkaA cewar sanarwar, Abba Hassan, wanda asalinsa ɗa Jihar Borno ne, ya gudu daga gidan yarin a ranar 31 ga watan Oktoba, bayan kotu ta yanke masa hukuncin kisa.
DSP Abdulkarim, ya roƙi jami’an tsaro, direbobi, sarakunan gargajiya, ’yan banga da al’ummomin Jihar Yobe da maƙwabtan jihohi da su taimaka da bayanai da za su taimaka wajen sake kama shi.
Ya kuma gargaɗi jama’a da kada su kusanci fursunan da ya tsere, domin hakan na iya zama hatsari.
“Domin kare lafiyarku, idan kuka ga wani da kuke zargi shi ne, ku sanar da ofishin ’yan sanda mafi kusa ko gidan gyaran hali, ko kuma ku kira lambar 08038452982,” in ji sanarwar.