Hukumar Kula da Sufuri ta Jihar Kaduna tace shirin Bus Rapid Transit BRT da ake shirin kaddamarwa zai taimaka matuka wajen rage kudaden sufuri ga mazauna jihar, da zarar an fara aiwatar da shi.

 

Daraktan Hukumar, Injiniya Inuwa Ibrahim, ne ya bayyana hakan yayin wani taron tattaunawa da masu ruwa da tsaki da aka gudanar a Kada Hive da ke Kaduna.

 

An shirya taron ne domin wayar da kan jama’a game da shirin BRT, sannan matakan da aka dauka ya zuwa yanzu.

 

Taron an gudanar da shi ne domin sauraron ra’ayoyin al’umma kan yadda za a aiwatar da shi cikin nasara.

 

Injiniya Inuwa ya bayyana cewa tsarin BRT zai taimaka wajen rage cunkoson ababen hawa da kara tsaro da aminci, da kuma inganta rayuwar al’umma baki daya a Jihar Kaduna.

 

Ya tuna cewa kimanin watanni biyu da suka gabata ne Gwamna Uba Sani ya kaddamar da sama da motoci 100 masu amfani da iskar gas na CNG, wadanda za su rika zirga-zirga a cikin Birnin Kaduna, Zariya da Kafanchan, a wani bangare na kokarin gyara tsarin sufuri a fadin jihar.

 

Ya bukaci mahalarta taron su yada ilimin da suka samu zuwa cikin al’ummominsu domin kara fahimta da goyon bayan jama’a don nasarar wannan shiri.

 

A nasa bangaren, Ted Regino, shugaban Rebel Artic Joint Venture, wanda ke sa ido kan kwangilolin aikin, ya ce kamfaninsa ne ke lura da yadda ake gudanar da aikin.

 

Ya tabbatar da cewa za a kammala aikin BRT kafin shekarar 2027, tare da karin bayani cewa kamfaninsu ya taba aiwatar da manyan ayyuka a kasa da kasa, kuma hakan zai maimaitu a Jihar Kaduna.

 

A nata jawabin, Shugabar Jam’iyyar Matan Arewa, Hajiya Rabi Saulawa, ta yaba da wannan shiri, tana mai cewa zai rage wa mata wahalhalun sufuri, musamman wadanda ke yawan zirga-zirga zuwa asibitoci, kasuwanni, wuraren aiki da makarantu.

 

Wasu daga cikin mahalarta sun jaddada bukatar kulawa da kiyaye motocin, tabbatar da dorewar shirin, da kuma kawo karshen matsalar sayar da tikiti ba bisa ka’ida ba.

 

Taron ya samu halartar wakilai daga sashen sufuri, shugabannin addinai da na gargajiya, ’yan jarida da sauransu.

 

COV: Adamu Yusuf

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Sabon Tsarin Sufuri Na BRT Zai Rage

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

A cewarsa, ta hanyar wadannan shirye-shirye, kasar Sin ta nuna goyon baya mai dorewa ga kasashe masu tasowa kuma tana ba da gudummawa mai ma’ana ga ci gaban duniya a karkashin tsarin hadin gwiwar kasashe masu tasowa. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace October 31, 2025 Daga Birnin Sin Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC October 31, 2025 Daga Birnin Sin Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik
  • Gidauniyar IRM Da KADCHMA, Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna
  • An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka
  • Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya
  • Dan Majalisar Jema’a/Sanga, Daniel Amos, Ya Koma Jam’iyyar APC
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi