Aminiya:
2025-07-24@03:34:03 GMT

Ba zan yi musayar yawu da yara ba — Martanin Amaechi ga Wike

Published: 4th, June 2025 GMT

Tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi, ya bayyana dalilin da ya sa ya naɗa Nyesom Wike a matsayin Shugaban Ma’aikata a lokacin da yake Gwamnan Jihar Ribas, maimakon Kwamishinan Kuɗi.

Amaechi, ya ce ya zaɓi Wike ne a matsayin Shugaban Ma’aikata domin ya samu damar sanya ido a kansa.

Tinubu ya gana da Fubara a Legas Jami’an DSS sun kashe ’yan bindiga 45 a Neja

“Na so ya zama shugaban ma’aikata ne saboda na riƙa sanha ido a kansa.

“Ban ba shi kujerar kwamishinan kuɗi ba,” in ji Amaechi a wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na Arise da yammacin ranar Talata.

Wannan martanin ya biyo bayan kalaman Wike ne, wanda yanzu shi ne Ministan Babban Birnin Tarayya, inda ya yi martani kan wata magana da Amaechi ya yi a bikin cikarsa shekaru 60 a duniya.

Ya ce: “Dukaninmu muna jin yunwa.”

Wike ya ce Amaechi yana yunwarsa a fili kan lallai sai ya zama wani abu a siyasar Najeriya.

Sai dai Amaechi ya musanta zargin Wike na cewa shi ne ya taimaka masa ya zama gwamna.

“Ubangiji, tsohon gwamna Peter Odili, kotuna, da kuma al’ummar Jihar Ribas ne suka sa na zama gwamna,” in ji shi.

“Ka tambaye shi yadda ya sa na zama gwamna. Ina faɗin haka ne saboda bana so na yi musayar yawu da yara.”

Amaechi ya ƙara sukar Wike, inda ya ce a yanzu ba ya ganin girman kowa har waɗanda suka taimake shi a rayuwa.

“Ka ga shi ya naɗa kansa shugaban ma’aikata. Ya naɗa kansa gwamna. Ya yi wa kansa minista. Ya kuma yi wa kansa shugaban ƙaramar hukuma,” in ji Amaechi.

Amaechi ya ce bai ga amfanin yin cacar baki da Wike a bainar jama’a ba, domin hakan bai dace da shi ba.

“Ina faɗin haka ne saboda bana so na shiga cece-kuce da yara,” ya maimaita.

Rigima tsakanin tsoffin abokan siyasar biyu na ci gaba da jawo hankalin jama’a, musamman duba da tarihin siyasarsu a Jihar Ribas.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: martani Siyasa

এছাড়াও পড়ুন:

DAGA LARABA: Abubuwan da ya kamata yara su yi yayin hutun makaranta

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

A duk lokacin da aka ce an kammala zangon karatu, dalibai kan samu hutu don hutawa da yin wadansu abubuwa na daban da kuma ba su damar shakuwa da ’yan uwa da abokan arziki.

Kamar yadda masana harkar harkar ilimi suka saba fadi, yawan karatu kan taho da nashi irin matsalolin, ya kuma kamata a ce ana ware wa dalibai wasu lokuta na musamman don samun hutu daga karatun da suka koya.

NAJERIYA A YAU: Yadda tsadar taki ke hana noman masara da shinkafa DAGA LARABA: Makomar Siyasar Najeriya Bayan Rasuwar Shugaba Buhari

Shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi nazari ne kan abubuwan da ya kamata yara su ringa yi yayin hutun makaranta.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin da muka gaza biyan ma’aikata mafi ƙarancin albashi — Gwamnatin Borno
  • Gwamna Namadi Ya Amince Da Nadin Sabbin Sakatarori Guda Takwas
  • UNICEF Ya Bukaci Jihar Kano Ta Bai Wa Yara Muhimmanci A Kasafin Kudi
  • DAGA LARABA: Abubuwan da ya kamata yara su yi yayin hutun makaranta
  • Gwamna Namadi Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Hukumar Hisba Ta Jihar Jigawa
  •  Iran Ta Yi Kira Ga “FIFA” Da Ta Kori “Isra’ila” Daga Cikinta
  • UNICEF na zargin Gwamnatin Nijeriya da cin zarafin ƙananan yara
  • Majalisar Dattawa Za Ta Yi Zama Na Musamman Don Karrama Buhari 
  • Gwamna Namadi Ya Jinjinawa Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Bisa Ayyukan Raya Kasa
  • Mataimakiyar Shugaban Majalisar Dinkin Duniya Ta Jinjinawa Gwamnan Kano Bisa Ayyukan Cigaban Jihar