Aminiya:
2025-06-06@07:06:45 GMT

Ba zan yi musayar yawu da yara ba — Martanin Amaechi ga Wike

Published: 4th, June 2025 GMT

Tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi, ya bayyana dalilin da ya sa ya naɗa Nyesom Wike a matsayin Shugaban Ma’aikata a lokacin da yake Gwamnan Jihar Ribas, maimakon Kwamishinan Kuɗi.

Amaechi, ya ce ya zaɓi Wike ne a matsayin Shugaban Ma’aikata domin ya samu damar sanya ido a kansa.

Tinubu ya gana da Fubara a Legas Jami’an DSS sun kashe ’yan bindiga 45 a Neja

“Na so ya zama shugaban ma’aikata ne saboda na riƙa sanha ido a kansa.

“Ban ba shi kujerar kwamishinan kuɗi ba,” in ji Amaechi a wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na Arise da yammacin ranar Talata.

Wannan martanin ya biyo bayan kalaman Wike ne, wanda yanzu shi ne Ministan Babban Birnin Tarayya, inda ya yi martani kan wata magana da Amaechi ya yi a bikin cikarsa shekaru 60 a duniya.

Ya ce: “Dukaninmu muna jin yunwa.”

Wike ya ce Amaechi yana yunwarsa a fili kan lallai sai ya zama wani abu a siyasar Najeriya.

Sai dai Amaechi ya musanta zargin Wike na cewa shi ne ya taimaka masa ya zama gwamna.

“Ubangiji, tsohon gwamna Peter Odili, kotuna, da kuma al’ummar Jihar Ribas ne suka sa na zama gwamna,” in ji shi.

“Ka tambaye shi yadda ya sa na zama gwamna. Ina faɗin haka ne saboda bana so na yi musayar yawu da yara.”

Amaechi ya ƙara sukar Wike, inda ya ce a yanzu ba ya ganin girman kowa har waɗanda suka taimake shi a rayuwa.

“Ka ga shi ya naɗa kansa shugaban ma’aikata. Ya naɗa kansa gwamna. Ya yi wa kansa minista. Ya kuma yi wa kansa shugaban ƙaramar hukuma,” in ji Amaechi.

Amaechi ya ce bai ga amfanin yin cacar baki da Wike a bainar jama’a ba, domin hakan bai dace da shi ba.

“Ina faɗin haka ne saboda bana so na shiga cece-kuce da yara,” ya maimaita.

Rigima tsakanin tsoffin abokan siyasar biyu na ci gaba da jawo hankalin jama’a, musamman duba da tarihin siyasarsu a Jihar Ribas.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: martani Siyasa

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya gana da Fubara a Legas

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya gana da gwamnan Jihar Ribas da aka dakatar, Siminalayi Fubara, a gidansa da ke Legas.

Wannan ganawar na cikin ƙoƙarin warware rikicin siyasa da ya addabi jihar.

Jami’an DSS sun kashe ’yan bindiga 45 a Neja ’Yan sanda sun sake hana hawan Sallah a Kano

Fubara, ya samu saɓani da ubangidansa na siyasa, Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, bayan hauwansa mulki.

Saɓani kan ikon mallakar kuɗin jihar da naɗin muƙamai ya janyo rarrabuwar kawuna a cikin gwamnatin jihar da kuma majalisar dokokin jihar.

A watan Maris 2025, Shugaba Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a jihar Ribas tare da dakatar da Gwamna Fubara, mataimakiyarsa, da kuma ‘yan majalisar dokokin jihar baki ɗaya.

Ya naɗa tsohon Hafsan Soja, Vice Admiral Ibokette Ibas (mai ritaya), a matsayin kantoma da zai kula da harkokin jihar.

“Tun da rikicin ya ci gaba da faruwa, babu yadda za a yi gwamnati mai bin doka da ƙa’ida ta ci gaba,” in ji Shugaba Tinubu a wani jawabi da ya yi.

“Komai ya ta tsaya cak a jihar tun da aka fara rikicin.”

“Gwamnan… ya rushe majalisar dokoki tun ranar 13 ga wata. Disamban 2023, kuma har yanzu bai gyara ta ba,” in ji Tinubu.

“Duk ƙoƙarina na yin sulhu babu abin da ya sauya.”

Duk da cewa ba a bayyana cikakken bayani kan ganawar da suka yi ba, an ce hakan na cikin ƙoƙarin samar da zaman lafiya tsakanin ɓangarorin biyu.

Wannan ganawar ta biyo bayan wata ganawa da suka yi a Landan watanni da suka gabata.

Majalisar Tarayya ta goyi bayan matakin Tinubu, kuma ta buƙaci a kawo ƙarshen dokar ta-ɓaci cikin watanni shida tare da kafa kwamitin sulhu domin warware matsalar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Barazanar Yajin Aiki: Abuja da wasu jihohi 3 za su faɗa cikin duhu
  • Gwamna Uba Sani Ya Samu Goyon Bayan Mazauna Mahuta Bayan Warware Rikicin Filaye
  • A shekara 25, na kashe tiriliyan 161 wajen inganta lafiya a Afirka – Bill Gates
  • Ambaliyar Mokwa: An gano gawar yara 7, jama’a na neman agaji
  • Babban Zauren MDD Ta Zabi Kasashen Congo Da Liberian Na Zama Mambobi A Kwamitin Tsaro
  • Tinubu ya gana da Fubara a Legas
  • Nukiliya : Iran za ta bayar da amsa ga shawarar Amurka cikin kwanaki masu zuwa
  • Gwamnn Zamfara Ya Ba Ma’aikata Da ‘Yan Fansho Barka Da Sallah
  • Bello Yabo Ya Je Wajen Wa’azi Da Bindiga A Sakkwato, Ya Ce Ya Shirya Kare Kansa