Hatsarin kwale-kwale ya yi ajalin mutum 7 a Sakkwato
Published: 4th, June 2025 GMT
Wasu mutum bakwai sun rasa ransu sakamakon hatsarin kwale-kwale lokacin da suke tafiya daga kauyen Gidan Husaini zuwa Gwargawu na karamar hukumar Shagari a jihar Sakkwato ranar Litinin.
Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a lokacin da mamatan ke tafiya a wani kogi, lamarin da ya jefa mutanen yankin cikin jimami da alhini.
Ba a dai bayyana sunayen wadanda suka rasun ba, amma hukumomi a yankin sun tabbatar da cewa dukkan mamatan ’yan asalin kauyen na Gidan Husaini ne.
Ambaliyar Mokwa: Yawan mutanen da suka salwanta ya haura 700 Babbar Sallah: Farashin kayan miya ya yi tashin gwauron zaboDa ya jagoranci wata tawagar gwamnatin jihar domin yin ta’aziyyar mamatan, Kwamishinan Kudi na jihar, Muhammadu Jabbi Shagari, ya bayyana hatsarin a matsayin rashi ga ilahirin mazauna yankin, jihar da ma al’ummar Musulmi baki daya.
Sai dai Kwamishinan ya yi kakkausan gargadi ga matuka kwale-kwalen a kan yin lodin da ya wuce kima, inda ya ce rayuwar mutane ta fi komai za a samu muhimmanci.
Sai dai hatsarin ya sake fito da damuwar da ake da ita kan harkar sufuri ta ruwa a yankunan karkarar jihar, inda mutane suka dogara da kwale-kwalen saboda karancin jiragen ruwa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: hatsarin kwalekwale Sakkwato kwale kwale
এছাড়াও পড়ুন:
Sallah: ’Yan sanda sun yi alƙawarin tabbatar da tsaro a Gombe
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, ta shirya tsare-tsaren tsaro domin ganin an yi Sallar Idi cikin kwanciyar hankali da zaman lafiya.
Kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya bayyana cewa za a tura ’yan sanda da sauran jami’an tsaro zuwa filayen Idi, Masallatai, da wuraren taro domin kula da tsaro da zirga-zirgar jama’a.
Ambaliyar Mokwa: An gano gawar yara 7, jama’a na neman agaji Kotu ta aike da ɗan Tiktok gidan yari kan yin shigar mata a KanoZa a sanya ido sosai a manyan hanyoyi musamman waɗanda ke kai wa zuwa wuraren sallah, domin rage cunkoso da sauƙaƙa zirga-zirgar jama’a.
An ware ƙofofin shiga da fita a filayen Sallah domin a riƙa duba mutane da kayan da suke ɗauke da su.
Rundunar ta kuma roƙi jama’a da su bi waɗannan ƙa’idoji domin kauce wa jinkiri.
’Yan sandan sun gargaɗi mutane da ka da su ajiye motoci ba bisa ƙa’ida ba, sannan su kaucewa yin salla a tsakiyar hanya, ko toshe hanyoyin fita.
Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, ya roƙi mutane da su bayar da haɗin kai wajen bin doka, tare da kasancewa masu lura da duk wani abu da zai kawo barazana.
Ya kuma gargaɗi masu laifi da su guji duk wani abu da zai jawo tashin hankali a jihar.
Hakazalika, ya taya al’ummar Gombe murnar Sallar Idi, tare da tabbatar musu cewa ’yan sanda za su ci gaba da kare lafiyar jama’a domin a yi bukukuwan sallah cikin kwanciyar hankali.