Guardian: Isra’ila Tana Kai Wa Makarantun Dake Dauke Da ‘Yan Gudun Hijira a gaza Hari, Tana Sane Da Hakan
Published: 3rd, June 2025 GMT
Jaridar Guardian ta ta kasar Birtaniya ta bada labarin cewa, Hare-haren da sojojin HKI su ka kai kan wata makaranta, inda yan gudun hijira Falasdinawa suke samun mafaka da gangan suka yi shi, suna sane, kuma a halin yanzu suna Shirin kai wa wasu makarantun guda 4 hare-hare nan gaba.
Jaridar ta kara da cewa: Isra’ila ta ayyana wasu Karin makarantu wadanda Falasdinawa suke samun mafaka a cikinsu domin kai musu hare-hare a nan gaba.
A cikin watanni da suka gabata sojojin mamayar sun kai hare-hare akan wasu gine-ginen 6 wadanda suka kasance makarantu ne, wadanda Falasdinawa maza da mata da yara suka maidasu wuraren fakewa daga hare-haren sojojin HKI, suka kai mutane 120 ga shahada.
A ranar Litinin da ta gabata ce, sojojin mamayar suka kai wani harin a kan makarantar “A’ishiyya” wacce ta zama sansanin ‘yan gudun hijira a garin Deir-Balah’ na tsakiyar Gaza. Suka kuma kai falasdinawa da dama ga shahada.
Amma suka bada sanarwan cewa, ‘yan ta’adda ne suke fakewa a cikin makarantar, ba tare da sun gabatar da wata shaida ta tabbatar da hakan ba.
A bisa wani rahoton na MDD ta fitar, ta ce kaso 95% na makarantun Gaza, sun lalace, a yayin da wasu kimani 400 su ka rushe gaba daya saboda hare-haren sojojin yahudawan. A ranar 26 ga watan Mayu da ya shude ne, sojojin HKI suka kai hare-harei a kan makarantar “Fahmi-Jarjawi” da take cike da ‘yan gudun hijira wanda shi ma ya yi sanadiyyar shahadar Faladinawa da dama.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Al’ummar Fegin Mahe Sun Yi Zanga-zanga Kan Kisan Jama’a Da ‘Yan Bindiga Ke Yi
Daruruwan mazauna kauyen Fegin Mahe da ke yankin Ruwan Bore a karamar hukumar Gusau ta Jihar Zamfara, sun gudanar da zanga-zanga a gaban Gidan Gwamnati da ke Gusau, inda suka bukaci gwamnatin jihar ta dauki matakin gaggawa kan kisan gilla da ‘yan bindiga ke yi a yankinsu.
Masu zanga-zangar sun rike takardu masu dauke da rubuce-rubuce kamar su: “Muna bukatar zaman lafiya a yankunanmu” da “Gwamnati ta cika alkawarin da ta dauka”.
A cewar mazauna kauyen, harin ya faru ne da safiyar ranar Laraba, lokacin da wasu ‘yan bindiga dauke da manyan makamai suka afka wa kauyen, inda suka rika harbin mai-kan-uwa-da-wabi.
Al’ummar yankin sun bayyana harin a matsayin daya daga cikin mafi muni da suka taba fuskanta a ‘yan shekarun nan, wanda ya bar su cikin tsoro da fargaba.
Masu zanga-zangar sun ce manufarsu ita ce jawo hankalin gwamnati kan tabarbarewar tsaro a yankin da kuma bukatar daukar matakin gaggawa don dakile kisan fararen hula da ake ta yi ba kakkautawa.
Sun kuma koka da cewa har yanzu akwai gawarwakin wasu daga cikin mutanen da aka kashe a dajin, amma babu wanda ke iya dauko su saboda tsoron sake fuskantar hari daga hannun ‘yan bindigar.
Har zuwa lokacin da ake hada wannan rahoto, ba a samu wata sanarwa ko martani daga gwamnatin jihar ba dangane da harin ko kuma zanga-zangar da aka gudanar.
Daga Aminu Dalhatu