Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6%
Published: 3rd, June 2025 GMT
Yau Talata, kungiyar masu jigilar kayayyaki da sayayya ta kasar Sin ta gabatar da alkaluman watanni 4 na farko na bana, wadanda suka nuna cewa, a watan Afrilu, sha’anin jigilar kayayyaki ya bayyana inganci da boyayyen karfi, kuma duk da kalubaloli da matsin lamba daga ketare da aka fuskanta, ya tafi yadda ya kamata tare da samun bunkasuwa.
Kazalika, yawan hajojin da aka yi jigila yana cikin wani yanayi mai dorewa, bisa la’akari da yadda jigilar kayayyaki ta amfani da layin dogo da hanyoyin mota ke tafiya yadda ya kamata, kana ana samun saurin bunkasuwar jigilar kayayyaki da ta hada mabambantan hanyoyi. Alkaluman sun kuma nuna cewa, daga watan Janairu zuwa na Afrilu, yawan hajojin da aka yi jigila ta hanyar layin dogo ya karu da kashi 3.6 cikin kashi 100 bisa na makamancin lokacin a bara, adadin na hanyoyin mota ya karu da kashi 5 cikin kashi 100, kana yawan kwantanonin da aka yi jigilar su ta amfani da jirgin kasa da na ruwa tare, ya wuce miliyan 5.38, wanda ya karu da kashi 19.1 cikin kashi 100 bisa na makamancin lokacin a bara. Nauyin yawan sakwanni da aka yi jigila ya kai fiye da ton miliyan 3, adadin ya karu da kashi 13 cikin kashi 100 bisa na makamancin lokacin bara. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: jigilar kayayyaki ya karu da kashi
এছাড়াও পড়ুন:
Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne
Babban abin dubawa a nan shi ne ko mene ne hikimar tura irin wadannan bakin haure zuwa kasashen Afirka? Misali kamar bakin hauren da Amerika take son turawa Nijeria, ’yan asalin kasar Venezuela, ko kuma bakin hauren da Sudan ta kudu ta karba ’yan asalin Myammar, da Cuba da Vietnam, al’adunsu da harshensu sun sha banban da na ’yan Afirka. Sabo da haka babu wata alaka tsakanin juna.
To idan ba domin isgilanci da gadara ba, ta yaya Mr. Trump zai nemi tursasawa kasashen Afirka karbar irin wadannan bakin haure maimakon ya tasa keyarsu zuwa kasashensu na asali?(Lawal Mamuda)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp