Aminiya:
2025-09-17@23:17:34 GMT

Bom ɗin Boko Haram ya kashe fasinjoji 9 a tashar mota a Borno

Published: 2nd, June 2025 GMT

Mutane tara sun mutu wasu da dama sun jikkata sakamakon tashin wani abu mai fashewa da ’yan Boko Haram suka dasa a ƙauyen Mairari da ke Ƙaramar Hukumar Guzamala ta Jihar Borno.

Lamarin ya faru a wata tashar mota a kauyen, wanda ke da nisan kilomita 18 daga Karamar Hukumar Monguno da kuma kilomita 119 daga Maiduguri.

Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Borno, Abdulkarim Lawan, mai wakiltar yankin, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana shi a matsayin “rashin imani.”

Abdulkarim Lawal ya bayyana cewa waɗanda lamarin ya shafa mazauna yankin ne masu juriya da ke komawa gonakinsu a Mairari.

NAJERIYA A YAU: Mokwa: Tsakanin Taraddadin Rashin Matsuguni Da Jimamin Rashin ’Yan-Uwa Layya da hukunce-hukuncenta a Musulunci

Kafin yanzu, sau biyu ana sake tsugunar da mutanen yankin bayan sun yi gudun hijira, amma hare-haren Boko Haram na sake tilasta musu yin ƙaura.

Lawan ya yi kira ga sojoji da su ƙaddamar da ayyuka masu zafi domin ƙwato ɗauƙacin Ƙaramar Hukumar Guzamala, ciki har da Gudumbali da Mairari, waɗanda ya ce suna ƙarƙashin ikon ’yan ta’adda.

Shugaban majalisar ya ce, “Abin takaici ne yadda mutane tara daga cikin al’ummata masu juriya suka mutu sakamakon fashewar bom da aka dasa yayin da suke jiran shiga motocin haya a wata tashar mota a kauyen Mairari.”

Ya addu’ar samu rahama ga mamatan da kuma samun lafiya ga wadanda suka jikkata.

Ya yaba da ƙoƙarin sabon Kwamandan rundunar Operation Hadin Kai, Manjo-Janar Abdulsalam Abubakar, amma ya sake jaddada buƙatar gaggawa ta dawo da mulkin farar hula a yankunan da abin ya shafa.

A sauya wa Barikin Giwa wuri — Kungiyar Bale Galtimari

A wani labarin mai nasaba da hakan, Ƙungiyar Tuntuɓa ta Bale Galtimari ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta kawar da barikin sojoji na Giwa daga inda yake a Maiduguri.

Dakta Zanna Boguma, shugaban kungiyar, ya bayyana yadda Boko Haram ke kai hare-hare akai-akai ga barikin, lamarin da ke jefa rayuwar mazauna yankin fiye da miliyan daya cikin hadari a yankunan farar hula kamar Galtimari, Fori, da 122.

Ya lura cewa barikin, wanda ake kyautata zaton yana tsare da ’yan ta’adda, an kai masa hari akai-akai domin sakin su, a 2014, 2015 (sau uku), da 2019.

Ƙungiyar ta jaddada cewa bai kamata a gina manyan sansanonin sojoji a cikin al’ummomin farar hula ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Galtimari

এছাড়াও পড়ুন:

An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin

Hukumar jin daɗin jama’a ta Jihar Kwara tare da haɗin gwiwar Hukumar Gyaran Hali ta Najeriya sun kama wasu mabarata a titunan Ilorin, ciki har da wasu da aka samu da kuɗaɗen ƙasashen waje.

Daga cikin waɗanda aka kama akwai wani mabaraci mai suna Musa Mahmud daga Jihar Kano, wanda aka samu da takardar daloli.

Musa Mahmud ya shaida wa manema labarai cewa wani ne ya ba shi takardar Dala a Abuja.

Jami’ai sun bayyana damuwa kan yadda masu bara ke riƙe da kuɗaɗen da ba su dace da yanayin rayuwarsu ba.

Mutuwar majinyata: Asibitin Aminu Kano na roƙon KEDCO ya dawo da wutar lantarki Cire tallafin man fetur shi ne abin da ya dace —Sarki Sanusi II

“Za mu bincika asalin waɗannan kuɗaɗen da kuma dalilin da ya sa suke da su,” in ji Adebayo Okunola, shugaban cibiyar gyaran hali a Jihar Kwara.

Jami’an gwamnati sun kwashe kusan mutane 40 daga wuraren da suka haɗa da Tipper Garage, Offa Garage, Tank da Geri Alimi Roundabout.

Jami’an sun ce bakwai daga cikin waɗanda aka kama an taɓa kama su a baya, amma sun koma tituna bayan an sako su.

Kwamishinar jin daɗin jama’a ta jihar, Dakta Mariam Imam, ta ce adadin masu bara da aka kama ya ragu sosai idan aka kwatanta da na baya, inda ta ce suna sauya dabaru don su guje wa kama.

Ta roƙi jama’a da su daina ba wa masu bara kuɗi kai tsaye, su maida gudummawarsu ta hanyar wuraren  ibada da gidajen marayu.

Jami’an gyaran hali sun ce za a tilasta wa waɗanda aka kama su yi aikin tsaftace tituna a matsayin horo da kuma darasi.

Wasu daga cikin masu barar sun roƙi gwamnati da ta tausaya musu, ba su da wata hanyar rayuwa sai bara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaidai Dake Kasar Yamen
  • Kungiyar Kare Hakkokin Bil’Adama Ta Siriya Ta Bankado Karin Fararen Hula Da Aka Kashe A Rikicin Suweida
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • Burkina Faso: Masu Ikirarin Jihadi Sun Kashe Fararen Hula 50 A Cikin Watanni Hudu
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin