Bom ɗin Boko Haram ya kashe fasinjoji 9 a tashar mota a Borno
Published: 2nd, June 2025 GMT
Mutane tara sun mutu wasu da dama sun jikkata sakamakon tashin wani abu mai fashewa da ’yan Boko Haram suka dasa a ƙauyen Mairari da ke Ƙaramar Hukumar Guzamala ta Jihar Borno.
Lamarin ya faru a wata tashar mota a kauyen, wanda ke da nisan kilomita 18 daga Karamar Hukumar Monguno da kuma kilomita 119 daga Maiduguri.
Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Borno, Abdulkarim Lawan, mai wakiltar yankin, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana shi a matsayin “rashin imani.”
Abdulkarim Lawal ya bayyana cewa waɗanda lamarin ya shafa mazauna yankin ne masu juriya da ke komawa gonakinsu a Mairari.
NAJERIYA A YAU: Mokwa: Tsakanin Taraddadin Rashin Matsuguni Da Jimamin Rashin ’Yan-Uwa Layya da hukunce-hukuncenta a MusulunciKafin yanzu, sau biyu ana sake tsugunar da mutanen yankin bayan sun yi gudun hijira, amma hare-haren Boko Haram na sake tilasta musu yin ƙaura.
Lawan ya yi kira ga sojoji da su ƙaddamar da ayyuka masu zafi domin ƙwato ɗauƙacin Ƙaramar Hukumar Guzamala, ciki har da Gudumbali da Mairari, waɗanda ya ce suna ƙarƙashin ikon ’yan ta’adda.
Shugaban majalisar ya ce, “Abin takaici ne yadda mutane tara daga cikin al’ummata masu juriya suka mutu sakamakon fashewar bom da aka dasa yayin da suke jiran shiga motocin haya a wata tashar mota a kauyen Mairari.”
Ya addu’ar samu rahama ga mamatan da kuma samun lafiya ga wadanda suka jikkata.
Ya yaba da ƙoƙarin sabon Kwamandan rundunar Operation Hadin Kai, Manjo-Janar Abdulsalam Abubakar, amma ya sake jaddada buƙatar gaggawa ta dawo da mulkin farar hula a yankunan da abin ya shafa.
A sauya wa Barikin Giwa wuri — Kungiyar Bale GaltimariA wani labarin mai nasaba da hakan, Ƙungiyar Tuntuɓa ta Bale Galtimari ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta kawar da barikin sojoji na Giwa daga inda yake a Maiduguri.
Dakta Zanna Boguma, shugaban kungiyar, ya bayyana yadda Boko Haram ke kai hare-hare akai-akai ga barikin, lamarin da ke jefa rayuwar mazauna yankin fiye da miliyan daya cikin hadari a yankunan farar hula kamar Galtimari, Fori, da 122.
Ya lura cewa barikin, wanda ake kyautata zaton yana tsare da ’yan ta’adda, an kai masa hari akai-akai domin sakin su, a 2014, 2015 (sau uku), da 2019.
Ƙungiyar ta jaddada cewa bai kamata a gina manyan sansanonin sojoji a cikin al’ummomin farar hula ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Galtimari
এছাড়াও পড়ুন:
Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan
Shugaban Masar Abdel Fattah al-Sisi ya gana da Shugaban Eritrea Isaias Afwerki domin tattauna halin da ake ciki a yankin, Shugaba al-Sisi ya tabbatar da jajircewar Masar wajen tallafawa ‘yancin kai da kuma ‘yancin yankin Eritrea.
A yayin taron, wanda Ministan Harkokin Wajen Masar Badr Abdel-Aty da takwaransa na Eritrea, Osman Saleh Mohammed suka halarta, shugabannin biyu sun tattauna halin da ake ciki a yankin.
Sun tabbatar da hangen nesansu kan hanyoyin kawo karshen yakin a Sudan, suna masu jaddada bukatar tallafawa cibiyoyin gwamnati na kasa, musamman Sojojin Sudan, tare da kin amincewa da duk wani yunkuri na kafa hukumomi ko cibiyoyi masu kishiyantar gwamnati a kasar.
Shugaba al-Sisi ya jaddada matsayar Masar da kuma kokarin da take yi don kawo karshen yakin da kuma rage wahalhalun jin kai na al’ummar Sudan, ta hanyar yin aiki tare da abokan huldar Masar don tabbatar da hadin kan Sudan, mutuncin yankin, da kuma ‘yancin kan kasa.
A nasa bangaren, Shugaba Afwerki ya nuna matukar godiyarsa ga rawar da y ace Masar tana takawa karkashin jagorancin Shugaba El-Sisi, wajen karfafa zaman lafiya da kuma kokarin ci gaban yankin kusurwar Afirka da Gabashin Afirka. Ya yi maraba da fadada hadin gwiwar tattalin arziki da Masar da kuma karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu kan batutuwan kasa da kasa da na yanki masu amfani ga junansu.
Taron ya kuma yi magana kan sabbin abubuwan da suka faru a Somaliya, inda Shugabannin biyu sun jaddada kudurin kasashensu na amincewa da sanarwar hadin gwiwa da aka fitar a taron kolin Masar, Eritrea, da Somaliya a Asmara a watan Oktoban 2014, wanda ya tabbatar da wajibcin girmama ka’idoji da dokokin kasa da kasa, musamman ma cikakken yankin Somaliya da dukkan kasashen yankin.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Kutsen Na Isra’ila A Kudancin Kasar October 31, 2025 Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa October 31, 2025 Iran ta yi fatali da kalamman IAEA Kan Shirin Nukiliyarta October 30, 2025 Trump Ya Umarci Ma’aikatar Yakin Amurka Ta koma gwajin makaman nukiliya October 30, 2025 Isra’ila ta amince da fadada matsugunai a Yammacin Kogin Jordan October 30, 2025 Gaza: hare-haren Isra’ila sun kashe mutane 100 Cikin Kwanaki Biyu October 30, 2025 Sudan : Kasashen duniya na tir da cin zarafi a El-Fasher October 30, 2025 Iran Ta Jaddada Bin Hanyar Diflomasiya Ko Da A Lokacin Yaki Ne Amma Ba Zata Amince Da Bin Umarni Ba October 30, 2025 Qalibaf: Amurka Tana Yaudarar Duniya Da Zaman Lafiya, Alhalin Tana Ci Gaba Da Kai Harin Wuce Gona Da Iri October 30, 2025 Ci Gaba Da Killace Gaza Bayan Tsagaita Bude Wuta Ya Janyo Mutuwar Mutane 1000 A Yankin October 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci