Hon. Nasiru ya kara da cewa Gwamna Radda ya yi kokari wajen yaki da matsalolin tsaro wanda suka addabi Jihar Katsina, inda ya bayyana cewa ana samun sauki sosai a wannan bangare.

Ya ce gwamnati ta gyara makarantu da asibitoci a fadin Jihar Katsina, inda aka maida su na zamani tare da daukar ma’aikatan lafiya da kuma malaman makaranta da yawansu ya kai 7,000, wanda ya ce ko haka aka tsaye suna da hujja da dalilin mara masa baya.

Idan za a iya tunawa a makon da ya gabata ne, ‘yan majalisun tarayya guda 15 dukkansu na jam’iyyar APC suka ayyana Gwamna Radda a matsayin wanda za su goya baya a zaben 2027.

Sai dai kuma ana dora ayar tambaya kan wadannan ‘yan majalisu da cewa sun yi riga Malam Masallaci, domin kafin su yanke irin wannan hukunci ya kamata su tuntubi wadanda suke wakilta domin gudun tutsu ranar zabe.

Yanzu dai abin jira a gani shi ne, Gwamna Radda zai maida biki, ma’ana dai shi ma ya amince kowane dan majalisa ya dawo kujerarsa ba tare da hammaya ba? Lokaci alkali!

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Gwamna Radda

এছাড়াও পড়ুন:

Hana shigar da abinci da Isra’ila ta yi zuwa Gaza ‘laifi ne na yaki’: MDD

Jami’in kula da ayyukan jin kai na Majalisar Dinkin Duniya ya ce matakin da Isra’ila ta dauka na hana agajin abinci ga Falasdinawa da ke fama da yunwa a yankin Zirin Gaza da aka yi wa kawanya ya zama laifin yaki.

“Muna ganin abinci dake jibge a kan iyakoki kuma ba a ba da izinin shigar da shi ba a lokacin da jama’a a gefen iyakar ke fama da yunwa, a yayin da muke jin ministocin Isra’ila suna cewa sun ayin hakan ne don matsa lamba kan al’ummar Gaza,” in ji Mataimakin Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Tom Fletcher a wata hira a ranar Jumma’a.

Irin wannan na a matsayin laifin yaki ne,” in ji shi.

Baya ga hakan ma a cikin ‘yan kwanakin nan, sojojin Isra’ila sun kashe masu neman agaji da dama a lokacin da suke kokarin isa wurin rarraba kayan agaji a yammacin Rafah a karkashin tsarin Amurka da Isra’ila.

Tuni dai hukumomin agaji na kasa da kasa suka yi gargadin cewa shirin da Isra’ila ke yi na sarrafa rabon kayan agaji a zirin Gaza, ciki har da shawarar da Amurka ke marawa baya, zai kara wahalhalu a yankin Falasdinawa.

A baya-bayan nan ne dai shugaban hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya (UNRWA) ya yi Allah-wadai da sabon salon agajin da Amurka ke marawa baya a Gaza, yana mai cewa “wani cin zarafi” da ke faruwa a can.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah
  • Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike
  • 2027: Ƙungiyar Shekarau Ta Gindaya Sharaɗi Kafin Shiga Haɗakar Jam’iyyu
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ta Iran Ya Ce: Taron Kungiyar BRICS Zai Kawo Bunkasar Tattalin Arziki
  • MDD : Gaza na cikin bala’i mafi muni tun soma yaki a Zirin a Oktoban 2023
  • Gwamnatin Tinubu na amfani da talauci a matsayin makami — Atiku
  • Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
  • Hana shigar da abinci da Isra’ila ta yi zuwa Gaza ‘laifi ne na yaki’: MDD
  • ‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba