HausaTv:
2025-07-24@03:25:00 GMT

Nukiliya : Tehran ta soki rahoton IAEA da cewa bai da tushe

Published: 1st, June 2025 GMT

Iran ta soki sabon rahoton da shugaban hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA ya fitar, tana mai cewa rahoto ne dake kunshe da tuhume-tuhume mara tushe kan shirin nukiliyar kasar.

A wata tattaunawa ta wayar tarho da babban darektan hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA, ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya bayyana cewa, Tehran za ta mayar da martani ga duk wani matakin da bai dace ba daga kasashen Turai da Amurka.

Faransa, Jamus da kuma Ingila, tare da goyon bayan Washington, suna son yin amfani da wannan rahoto don aiwatar da wani tsari da zai ba da damar maido da takunkumin Majalisar Dinkin Duniya kan Iran.

A cikin rahoton nasa, Rafael Grossi ya bayyana cewa Iran ta inganta shirinta na inganta makamashin Uranium sosai, wanda ya hada da ingantawa zuwa kashi 60%, matakin da ya kai kusan kashi 90% da ake amfani da shi wajen kera makaman nukiliya.

Ya kuma zargi Tehran da rashin bayar da cikakken hadin kai ga hukumar.

Ya kuma ce “Iran ita ce kasa daya tilo da ba ta da makaman nukiliya da ke inganta uranium a wannan matakin.

Wannan rahoton dai na zuwa ne a yayin da ake shirin gudanar da taro na gaba na hukumar gudanarwar IAEA a ranar Litinin mai zuwa 8 ga watan Yuni a Vienna, inda za a tattauna batun nukiliyar Iran.

Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta sha nanata cewa inganta sinadarin Uranium zuwa kashi 60 cikin 100 na cikin tsarin da take da shi na kare hakkinta na nukiliya cikin lumana, msuamman a fannin masana’antu da kiwon lafiya.

Iran ta sha bayyana cewa tana bada hadin kai ga hukumar ta IAEA, amma kasar ta sha yin gargadi akan yadda hukumar ta IAEA ke amfani da siyasa da kuma zama ‘yar amshin shatan wasu kasashen yammacin duniya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ministocin Tsaron kasashen Rasha Da JMI Sun Hadu A Birnin Mosco

Ministocin tsaro na kasar Rasha ta JMI sun hadu a birnin Mosco don tattauna batun karfafa dangantakar tsaro a tsakaninsu a dai dai lokacinda al-amuran tsaro suke kara tabarbarewa a yankin kudancin Asiya.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto jakadan kasar Iran a Mosco yana fadar haka.

Kazem Jalali, ya bayyana cewa kasashe biyu suna kara zurfin dangantakarsu da juna a dai-dai kasashen biyu suke kara fuskantar matsinn lamba daga kasashen yamma musamman Amurka, da kuma HKI.

Kasashen biyu sun ga yakamata su kara dankon zumunci a tsakaninsu a fagen tsaro, bayan yakin kwanaki 12 wanda Amurka da HKI suka dorowa kasar Iran.

A wannan zuwan dai ministan tsaron JMI ya raka Dr Ali Larijani babban mai bawa jagoran juyin njuya hali musulunci shawara a ganawarsa da shugaba Vladmir Putin a fadar Krimlin a ranar Lahadi.

Kazem Jalali, ya bayyana cewa a wannan karon ma bangarorin biyu sun tattauna baton karfafa dangantakar tsaron kasashen biyu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Amince Da Nadin Sabbin Sakatarori Guda Takwas
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Jaddada Hakkinta Na Tace Sinadarin Uranium A Cikin Kasarta
  • Pezeshkian: Tunanin Kawo Karshen Shirin Nukiliyar Iran Ya Yi Kama Da Tabuwa
  • Jami’an Kasashen Rasha, China, Iran Sun Gudanar Da Taron Hadin Gwiwa A Tehran
  •  Netanyahu: Ba Za Mu Daina Yakin Gaza Ba
  • Yanzu-Yanzu: Majalisa Ta Amince Wa Tinubu Ciwo Bashin Dala Biliyan 21
  • Hukumar Kashe Gobara Ta Jihar Kwara Ta Taimaka Wajen Hana Lalacewar Wani Bene A Ilorin
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce; Iran Ba Zata Bar Tace Sinadarin Uranium Ba
  • Jami’in Shari’ar Kasa Da Kasa Ya Bayyana Cewa: Harin Da Aka kai Kan Iran Babban Laifi Ne
  • Ministocin Tsaron kasashen Rasha Da JMI Sun Hadu A Birnin Mosco