Nukiliya : Tehran ta soki rahoton IAEA da cewa bai da tushe
Published: 1st, June 2025 GMT
Iran ta soki sabon rahoton da shugaban hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA ya fitar, tana mai cewa rahoto ne dake kunshe da tuhume-tuhume mara tushe kan shirin nukiliyar kasar.
A wata tattaunawa ta wayar tarho da babban darektan hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA, ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya bayyana cewa, Tehran za ta mayar da martani ga duk wani matakin da bai dace ba daga kasashen Turai da Amurka.
Faransa, Jamus da kuma Ingila, tare da goyon bayan Washington, suna son yin amfani da wannan rahoto don aiwatar da wani tsari da zai ba da damar maido da takunkumin Majalisar Dinkin Duniya kan Iran.
A cikin rahoton nasa, Rafael Grossi ya bayyana cewa Iran ta inganta shirinta na inganta makamashin Uranium sosai, wanda ya hada da ingantawa zuwa kashi 60%, matakin da ya kai kusan kashi 90% da ake amfani da shi wajen kera makaman nukiliya.
Ya kuma zargi Tehran da rashin bayar da cikakken hadin kai ga hukumar.
Ya kuma ce “Iran ita ce kasa daya tilo da ba ta da makaman nukiliya da ke inganta uranium a wannan matakin.
Wannan rahoton dai na zuwa ne a yayin da ake shirin gudanar da taro na gaba na hukumar gudanarwar IAEA a ranar Litinin mai zuwa 8 ga watan Yuni a Vienna, inda za a tattauna batun nukiliyar Iran.
Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta sha nanata cewa inganta sinadarin Uranium zuwa kashi 60 cikin 100 na cikin tsarin da take da shi na kare hakkinta na nukiliya cikin lumana, msuamman a fannin masana’antu da kiwon lafiya.
Iran ta sha bayyana cewa tana bada hadin kai ga hukumar ta IAEA, amma kasar ta sha yin gargadi akan yadda hukumar ta IAEA ke amfani da siyasa da kuma zama ‘yar amshin shatan wasu kasashen yammacin duniya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
Fitattun dalibai akalla 12 ne daga makarantun gwamnati suka samu guraben tallafin karatun sakandare a ƙarƙashin Asusun Tallafin Karatu na Jihar Kwara (Kwara-ETF).
A wajen taron gabatarwa ga waɗanda suka fara cin moriyar shirin, Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq ya bayyana cewa ci gaban harkar ilimi a Najeriya abu ne mai tsada kuma ya zama wajibi kowa ya bayar da gudummawarsa.
Ya roƙi masu masu hannu da shuni da kungiyoyi masu zaman kansu da su tallafa wajen gina makarantu ko kuma su ɗauki nauyin daliban da suka nuna bajinta da jajircewa a harkar karatu.
A cewarsa, an zabo daliban 12 ne sakamakon bajintar da suka nuna a matakai daban-daban na tantancewa da Kwara ETF ta gudanar.
Gwamnan ya bayyana cewa tallafin ya kunshi dukkan kuɗin da ake buƙata a karatun sakandaren daliban.
“Muna kira da jama’a su ba da gudummawa da kuma ɗaukar nauyin ɗalibai. Kada a bar wannan aiki ga gwamnati da iyaye kadai. Ilimantar da ‘ya’yanmu hakki ne da ya rataya a kanmu gaba ɗaya,” in ji Gwamna.
Ya yaba da tsarin zaɓen kuma ya taya waɗanda suka yi nasara murna.
A nata jawabin, Babbar Shugabar Kwara ETF, Oluwadamilola Amolegbe, ta ce daliban 12 sun fito ne daga cikin jerin ɗalibai 640 da aka fara tantancewa bisa cancanta.
Ta bayyana cewa tsarin zaɓen ya fara ne da rubuta jarabawa ga dukkan daliban firamare na aji shida da suka amfana da shirin KwaraLEARN na koyon fasahar zamani, har zuwa lokacin da aka kammala tantancewa.
Ali Muhammad Rabi’u